Connect with us

Labarai

An tsare wani ma’aikacin man fetur bisa zargin satar naira miliyan 3.4

Published

on

Wani ma’aikacin man fetur mai suna Waliu Olamilekan ɗan shekaru 39 a duniya a ranar Litinin ɗin da ta gabata an tsare shi a kotun Badagry da ke Legas bisa zargin satar Naira 3,464,000 a tashar BFO da ke Badagry.

Wanda ake tuhumar da ba a san adireshin sa ba a san shi ba yana fuskantar shari’a kan tuhume-tuhume uku da suka haɗa da shiga ba bisa ƙa’ida ba, ɓarna da kuma sata, wanda ya ƙi amsa laifinsa.

Mai gabatar da ƙara, Isfekta Ayodele Adeosun ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne a ranar 9 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:30 na safe a Pipeline, Araromi-Ale, Badagry Expressway, Lagos.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun banka wa jirgin ruwan satar ɗanyen man fetur wuta

Adeosun ta ce wanda ake zargin ya kutsa cikin ofishin manajan gidan rediyon, Misis Titilope Falola, mai shigar da ƙarar tare da ƙwace kuɗin.

“Ya lalata tagar da kuɗinsa ya kai Naira 45,000, babban ɗakin da kuma aljihun ofishin Manaja.

“Wanda ake tuhumar ya kuma saci zunzurutun kuɗi har naira miliyan 3, 464,000, mallakin gidan ajiyar kaya na BFO. “

’Yan sanda sun samu nasarar ƙwato kuɗaɗen da aka sace daga inda ya ɓoye.

Laifukan sun ci karo da sashe na 307, 339 da 287 na dokar laifuka ta jihar Legas, 2015,” in ji shi.

Alƙalin kotun, Mista T.A Popoola, ya bayar da belin wanda ake ƙara a kan kuɗi N1, 000,000 tare da masu tsaya masa guda biyu.

Popoola ya ce ya kamata ɗaya daga cikin waanda za su tsaya masa ya gabatar da shaidar bayanan asusun da ya kai Naira miliyan ɗaya da kuma tabbatar da adireshin haraji na shekaru uku.

Ta ɗage ci gaba da sauraron ƙarar har zuwa ranar 21 ga watan Agusta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like