Connect with us

Boko Haram

An sake ceto ƴan matan Chibok biyu a Jihar Borno

Published

on

Rundunar sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa ta ƙara ceto ƴan matan Chibok guda biyu a Jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya. Babban kwamandan Operation Hadin Kai Manjo Janar Christopher Musa ne ya tabbatar da hakan inda ya ce irin matsin lambar da ƴan Boko Haram ɗin ke fuskanta ne ke sawa suna guduwa suna barin ƴan matan Chibok ɗin.

Manjo Janar Musa ya shaida wa BBC cewa ɗaya daga cikin matan da aka ceto an same ta ne a ranar 29 ga watan Satumba inda aka same ta da yara huɗu.

Yana Pogu, ita ce ta 19 a jerin ƴan matan na Chibok da aka yi garkuwa su.

Ya ce akwai maza biyu da kuma ƴan biyu mata da ta haifa inda ya ce ƴan biyun jarirai ne sabuwar haihuwa.

Ya bayyana cewa dakarun Birged na 21 ne suka gano ta a samamen da suka kai a yankin na ƙauyen na Mairari da ke Ƙaramar Hukumar Bama.

Sa’annan a a ranar 2 ga watan Oktoba, an gano Rejoice Sanki wadda sunanta ne na 70 a jerin yan matan na Chibok da aka yi garkuwa da su.

Ita kuma an gano ta ne yankin Kawuri da ke Ƙaramar Hukumar Konduga tare da ƴayanta biyu.

Kwamandan ya tabbatar da cewa a bana 2022 kawai, an samu nasarar ceto ƴan matan Chibok 11.

Tun a 2014 ne dai ƴan Boko Haram suka sace ƴan mata a makarantar gwamnati ta mata da ke Chibok inda suka kwashe mata 276.

Sai dai tun daga lokacin zuwa yanzu sama da mata 170 suka koma ga iyalansu.

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Boko Haram

Boko Haram sun kashe manoma 15 a jihar Borno

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan ƙungiyar Boko Haram ne sun kashe aƙalla mutane 15 a hare-haren da suka kai kan wasu ƙauyuka biyu a ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

Kamar yadda rahoton Daily Trust ta ruwaito, ‘yan ta’addan sun kai farmaki ƙauyen Ƙofa ne da tsakar dare inda suka fara harbe-harbe ba da daɗewa ba, wanda har zuwa safiyar Juma’a.

An tattaro cewa maharan sun kuma kai hari a ƙauyukan Molai Kura da Molai Gana inda suka yi ta yanka mutane da ba a tantance adadinsu ba.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan Boko Haram suka yiwa masunta 29 kisan gilla, suka jikkata 9 a Gamborun Ngala

Lamarin dai ya sa mazauna yankin da dama sun ƙauracewa gidajensu zuwa wani daji da ke kusa.

Wani jigo a ƙungiyar ’yan banga, Bukar Ali-Musty, ya shaida wa jaridar cewa manoman na aikin gonakinsu ne a kusa da Molai, da ke wajen birnin Maiduguri, a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, inda ‘yan tada ƙayar bayan suka kai musu hari suka sare kawunansu.

“Aƙalla gawarwaki 15 ne aka kwashe a safiyar yau, an kai hare-haren ne jiya (Alhamis).

“An sare kan manoma bakwai a lokacin da suke aikin gonakinsu, sannan maharan sun kuma yanka wuya ga wasu fararen hula takwas da ba su da illa a gidajensu,” in ji shi.

Wani memba a ƙungiyar ‘civilian JTF’ da ke cikin tawagar da aka kwashe, ya nuna damuwarsa kan hare-haren, yana mai cewa dole ne duk masu ruwa da tsaki su farka don ganin ba a ci gaba da faruwa ba.

“Abin takaici ne ci gaba idan aka yi la’akari da ci gaban da muka samu a cikin watanni ba tare da an kai wa al’umma hari ba.

“Ina can da safe. Ba zan iya tunanin ganin an yanka ’yan uwana kamar rago ba.

Dukkanin gawarwakin da muka ƙwato an same su ne a cikin kwance cikin jini, kuma ina ganin dukkanmu muna buƙatar mu tashi tsaye domin tunkarar wannan maƙiyin zaman lafiya,” inji majiyar.

Continue Reading

Boko Haram

ISWAP ta kashe mutane uku da jikkata sojoji takwas a Borno

Published

on

Aƙalla ‘yan gudun hijira guda uku ne aka kashe tare kuma da jikkata wasu 13 ciki har da sojoji guda takwas a wasu mabambantan hare-hare da ƙungiyar ISWAP ta kai ƙaramar hukumar Damboa na jihar Borno.

An ruwaito cewa lamarin ya faru ne lokacin da ‘yan gudun hijira guda huɗu da ke zama a sansanin Lowcost a Damboa suka fita domin neman itacen hura wuta lokacin da mayaƙan suka buɗe musu wuta, inda suka kashe uku nan take yayin da sauran mutane kuma suka tsere da raunuka.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tun da farko ISWAP ɗin sun jikkata wasu sojoji da kuma fararen hula yayin wani hari da suka kai yankin Talala a ranar Talata duk a Damboa.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da cewa sojoji sun kashe mayaƙan na ISWAP da dama a wani hari da suka kai musu.
Majiyar ta ce wani jrgin sama na sojoji ya je Damboa a jiya Alhamis, inda ta ɗebo sojoji da suka jikkata zuwa Maiduguri domin yi musu magani.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like