Rahotanni daga Legas na cewa wasu fusatattun jama’a sun kashe wasu mutum biyu da ake zarginsu da yin sata a wurin mai POS.
Mai magana da yawun ƴan sanda reshen Jihar Legas SP Benjamin Hundeyin ne ya tabbatar da hakan a shafinsa na Twitter inda ya ce lamarin ya faru ne a Unguwar Igando inda fusatattun jama’ar da ke wurin suka yi dirar mikiya kan waɗanda ake zargin inda suka ƙona su ƙurmus.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/10/Screenshot_20221002-155636_Facebook-1024x989.jpg)
Ko da ƴan sanda suka isa wurin, jama’ar da suka yi wannan aika-aika sun watse.
SP Hundeyin ya bayyana cewa tuni aka soma gudanar da bincike.
Leave a Reply