Amfani da tayoyin jabu da gudun wuce ƙa’ida ne ke kashe yawancin masu ababen hawa – FRSC

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) ta yi gargaɗin cewa ci gaba da amfani da tayoyin jabu, da gudun wuce kai’ida da kuma laifukan ‘yan fashi, fashi da garkuwa da mutane a manyan tituna, yanzu sune manyan hanyoyin kashe-kashen masu ababen hawa a ƙasar nan.

Domin rage yawan waɗanda abin ya shafa da kuma rage kashe-kashe a tituna, hukumar ‘Road safety’ ɗin ta gargaɗi masu ababen hawa da su guji yin amfani da tsofin tayoyin da suka mutu, da shaye-shayen barasa fiye da kima da a lokacin tafiye-tafiye da daddare don gudun ka da masu garkuwa da mutane da ‘yan fashi su kai musu hari.

KU KUMA KARANTA: Mutane 37 sun mutu a hatsarin mota tsakanin Damaturu zuwa Maiduguri

Shugaban Hukumar FRSC, Dauda Ali Biu ne ya bayyana haka a Ifaki Ekiti, ƙaramar hukumar Ido/Osi ta jihar Ekiti a ƙarshen mako a yayin taron manyan motocin alfarma na shekarar 2023 domin wayar da kan masu ruwa da tsaki kan shawarwarin tsaro a manyan tituna ƙasa.

Waɗanda suka halarta a wajen taron sun haɗa da jami’an jiha da na ƙananan hukumomi, sarakunan gargajiya, malaman addini, ƙungiyoyin Direbobi, masu tuƙa babura, ‘yan kasuwa, jami’an tsaro da dai sauransu.

Biu, wanda kwamandan rundunar Corps Charles Edem ya wakilta, wanda ya yi magana game da kayayyakin da ba su da inganci, ya gargaɗi masu amfani da hanyar da su riƙa sayan tayoyi masu inganci a ko da yaushe, saboda haɗarin da ke tattare da amfani da “tsoffin tayoyi” ya fi ban tsoro fiye da bambancin farashin.

“Akwai kuma buƙatar samun isasshen hutu kafin da kuma lokacin doguwar tuƙi. Shaye-shaye na sanya wasu Direbobi su kasance masu riƙon sakainar kashi da gudun wuce ƙa’ida yayin tafiya da daddare.

“Al’amuran da suka shafi gudu, rashin tsaro da amfani da tayoyin jabu a yanzu su ne suka fi kashe masu ababen hawa a manyan hanyoyinmu kuma dole ne mu kauce musu don kare rayukanmu,” inji Biu.

A cikin shirin, inda aka yi wasan kwaikwayo na nuna rashin jin daɗi a cikin tuƙin ganganci, Kwamandan Sashen na Jihar Ekiti, Olusola Joseph, ya bayyana cewa gudun wuce ƙa’ida ya kai kashi 25.8 na mace-mace a hanyoyin Najeriya.

Joseph wanda Mataimakinsa Kwamandan Rundunar, Olajide Mogaji ya wakilta, ya ce, “Bayanan da aka samu a hukumar sun nuna cewa gudun wuce ƙa’ida ne ke haifar da haɗarurruka a kan tituna da kuma mace-mace a ƙasar nan wanda ke haifar da ƙalubalen da ake fuskanta wajen tafiyar da ababen hawa a Najeriya.

Joseph ya yi kira ga membobin ƙungiyar ma’aikatan sufurin mota ta Najeriya, kungiyar ma’aikatan sufurin jiragen ruwa ta Najeriya da sauran masu motoci da babura masu zaman kansu da su haɗa hannu da hukumar FRSC domin rage mace-macen da ake samu a manyan tituna.


Comments

One response to “Amfani da tayoyin jabu da gudun wuce ƙa’ida ne ke kashe yawancin masu ababen hawa – FRSC”

  1. […] KU KUMA KARANTA: Amfani da tayoyin jabu da gudun wuce ƙa’ida ne ke kashe yawancin masu ababen hawa – FRSC […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *