Connect with us

Doka

Abinda ya sa aka janye dokar hana ‘yan adaidaita hawa manyyan tituna a Kano

Published

on

Daga Shafa’atu DAUDA, kano

A yammacin Laraba ne gwamnatin jihar Kano ta janye dokar takaita hanyoyin bi ga matuka babura masu kafa uku da aka fi sani da Adaidaita sahu, ‘yan awowi kaɗan bayan da dokar ta fara aiki da safiyar ranar.

Shugaban Hukumar karota Baffa Babba Dan agundi ne ya bayyana sanar da janye dokar yayin wani taro da yayi da manema labarai a ofisoshin sa a Kano.

Ya ce “mun janye dokar ne saboda biyayyar da ‘yan adaidaita suka yi ga dokar da kuma kokawar da al’ummar jihar suka yi akan dokar”.

Tun da fari dai an gudanar da zanga zangar rashin goyon bayan dokar na takaita wa ‘yan adaidaita sahu hanyoyin da zasu bi, inda wasu matasa sun ka hau kan titin Hadeja Road kusa da Kwanar Dakata don nuna tirjiya ga dokar hana baburan Adaidaita Sahu bin wasu titunan Jihar.

Matasan da suka hada da matuka baburan da kuma mazauna yankin da suka hada da ɗaliban makaranta da ’yan kasuwa da sauran jama’ar yankin inda suka rufe kan titin suka hana sauran ababen hawa bin hanyar.

Baya ga haka kuma matasan sun yi ta ihu tare da furta kalaman Allah-wadai da matakin na Gwamnatin Jihar ta Kano.

Wasu daga cikin masu zanga-zangar sun yi amfani da wannan dama wajen jifan jami’an tsaro tare da ababen hawansu da duwatsu, yayin da wasu suka farfasa manyan motocin da gwamnatin Kano ta tanadar domin maye gurbin baburan masu ƙafa uku.

Haka kuma, ana cikin zanga-zangar sai ga wasu daga cikin motocin da Gwamnatin ta samar da suka maye gurbin baburan da ake yi wa lakabi da Kanawa Bus Service sun iso daidai wurin da ake zanga-zangar, nan da nan kuwa matasan suka fara jifan motocin da duwatsu inda suka farfasa gilasan motocin tare da yi wa fasinjojin da ke ciki rotse.

Sai dai kasancewar akwai isassun jami’an tsaro akan titin wanda aka ajiye su don ko-ta-kwana sun yi kokarin kwantar da tarzomar inda suka kama wasu daga cikin matasan wadanda suke zargin su ne da alhakin assasa zanga-zanga tare da tunzura matasan.

Wasu daga cikin ɗaliban makarantu da ke yankin sun shaida wa wakiliyar Neptune prime cewa sun shiga wannan zanga-zangar ce saboda rasa abin hawan da zai mayar da su gidajensu.

Wani dalibai mai suna Ahmad Ali ya ce, “Kasancewar jarrabawa muke yi ana tashinmu da karfe 11:00 na safe, to amma saboda rashin baburan Adaidaita Sahu gashi har yanzu karfe 12:30 muna kan titin, babu motocin da aka ce su za su dauke mu.
“A gaskiya Gwamnati ba ta kyauta mana ba. Kamata ya yi gwamnati ta yi abin a hankali ba wai kawai cikin kankanen lokaci ace za a kawo doka ta fara aiki ba.”

Shi ma wani matashi da ke cikin masu zanga-zangar wanda ya ki bayyana sunansa, ya shaida wa mana cewa sun yi zanga-zangar ne don sun rasa abin hawan da zai biya musu bukatunsu na sufuri.

“Kin San nan akwai Kasuwar Yankaba to muna yin amfani da baburan Adaidaita Sahu wajen daukar mana kayan gwari da muka saya zuwa wuraren kasuwancinmu, amma kin ga yau saboda wannan doka mun rasa abin da zai daukar mana kayan. Ga shi har rana ta yi,” inji shi.

Neptune prime ta tuntubi Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya ce ba shi da masaniya a kan abin da ke faruwa.
Sai dai ya ce da zarar ya bincika zai tuntunbe mu. Amma har zuwa lokacin hada wannan rahoton ba mu sami kira daga wajenshi ba.

Yanzu haka dai hankula sun kwanta biyo bayan matakin janye dokar da gwmanati jihar Kano tayi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda wata mace ta fille kan jaririnta da adda | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Doka

Kotu ta umarci jihar Ondo da ta biya diyyar naira miliyan 30 ga mutumin da ‘yan Amotekun suka harbe

Published

on

Ta kama mijinta yana lalata da ’ya’yan cikinsu

Wata babbar kotun Ondo da ke zamanta a Akure, a ranar Larabar da ta gabata ta umarci gwamnatin jihar Ondo da ta biya wani Oluwasegun Oluwarotimi kuɗi naira miliyan 30 a matsayin diyyar harbin bindiga da ya samu a wata arangama da jami’an tsaro na jihar, wanda aka fi sani da ‘yan Amotekun.

Oluwarotimi mai shekaru 36, mai tuƙa babur ne, wato ɗan okada ne lokacin da lamarin ya faru.

A nasa jawabin, Mai shari’a Adejumo ya bayar da umarnin a biya Oluwarotimi kuɗi naira miliyan talatin a matsayin diyya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NYSC ta biya diyya ga dangin ɗan bautar ƙasa da ya ɓata

Oluwarotimi, wanda a yanzu an yanke shi ne sakamakon harbin da aka yi masa ba bisa ka’ida ba,inda ya shigar da karar a gaban kotu.

“B bisa ka’ida ba a titin Araromi a ranar 9 ga watan Agustan 2021 a Akure, harbin da Amotekun ta yi ya saɓa wa hakkin ɗan Adam.

“Kotu ta umurci waɗanda ake ƙara da su hada kai su biya Naira miliyan 20 ga wanda ake kara a matsayin diyya na gaba daya da kuma Naira miliyan 10 a matsayin diyya ta misali,” in ji alkalin.

Continue Reading

Doka

An sanya dokar hana fita a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sanya dokar ta-ɓaci har zuwa faɗuwar rana don kaucewa taɓarɓarewar doka da oda, biyo bayan tattara sakamakon zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar da safiyar Litinin.

KU KUMA KARANTA: Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya lashe zaɓen Kano

Ya ce an yanke shawarar ne don hana ’yan daba su haifar da hargitsi a halin da ake ciki.

Kwamishinan ya yi kira ga jama’ar jihar da su kasance a cikin gida domin jami’an tsaro ba za su ƙyale kowa ko wata ƙungiyar da ke da niyyar haddasa fitina ba.

Continue Reading

Doka

Kotu ta sanya sharudɗa akan batun bada belin doguwa

Published

on

sharudɗan sune kamar haka:

Kotu ta haramtawa Alhassan Ado Doguwa zuwa mazaɓarsa ranar zaɓen ta gwamna da ‘yan majalisar jiha.

Wannan dai na cikin sharudɗa da babbar kotun tarayya ta sanya kafin bada belin Alhassan Ado Doguwa.

Ga dai ƙarin jerin sharudɗan da kotu ta sanya kafin bada belin.

1- Zai ajiye zunzurutun kuɗi har naira miliyan 500

2- Gabatar da sarki mai daraja ta ɗaya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

KU KUMA KARANTA: INEC ta cire sunan shugaban masu rinjaye, Doguwa daga jerin sunayen ‘yan majalisar wakilai

3- Gabatar da babban sakatare a gwamnatin jiha ko ta tarayya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

4- Zai ajiye Fasfo da sauran dukkanin takaddunshi na tafiya a kotu.

A karshe kuma kotu tace bazai halacci mazaɓarsa ba yayin zaɓen gwamna da yan majalisun jiha dake tafe.

Ko ya kuke kallon wannan batu?

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like