Connect with us

'Yansanda

Yadda ɗan damfara ya yaudari ’yan sandan Ngelzarma, da wasu mutane biyu: Labarin Bello Muhammad ​​da Sulaiman Garba

Published

on

Bello Muhammad mazaunin garin Ngelzarma ne, a ƙaramar hukumar Fune ta jihar Yobe, Najeriya. Yana gudanar da sana’ar cajin waya, inda mutane ke kawo wayoyinsu ayi musu caji, kuma su biya shi kuɗin aikin sa.

Wani ɗan damfara ya zo shagonsa, sai ya ga wata waya mai tsada, sai ya yanke shawarar cewa sai ya mallaki wannan wayar, har da wasu wayoyinma. Kai tsaye ya nufi ofishin ‘yan sanda, da rigar ciki ta ‘yan sandan Najeriya, da katin shaida na ƙarya.

Ya gabatar da kansa a matsayin CID a hedkwatar, kuma ya ba da rahoton cewa ya bi diddigin wata wayar da aka sace (Tracking) zuwa wani wurin cajin waya, inda a take suka ba shi umarnin ya je ya kawo wayar, da kuma mai kula da shagon wayar. Don haka ya je shagon Muhammad Bello ya gaya masa irin labarin da ya faɗawa ‘yan sanda cewa ya bi diddigin wata waya da aka sata zuwa shagonsa, zai kai Muhammad ​​da wayar ofishin ‘yan sanda.

Muhammad da sanin cewa bai aikata komai ba, ya bishi har ofishin ‘yan sanda da ke bayan gari. ‘Yan sanda ba su ji ta bakin Muhammad ​​ba, suka cire masa kaya da ‘yan mukullinsa da wasu kayansa sannan suka kulle shi.

Muhammad Bello, mai shagon charjin waya

CID na bogi ya ɗauki wayar, da nufin fita daga ofishin ‘yan sandan, inda ya ba su lambar waya ta bogi tare da katin shaidar ƙarya. Da aka tambaye shi ko yana da wata shaida ta bin diddigin, (Tracking certificate), sai ya ce yana tare da sajan nasa a cikin gari, kuma zai je ya kawo.

Ya ɗauki babur ya wuce kai tsaye shagon Muhammad, ya umarci mai tsare shagon wayar daya kawo wayar maigidansa, suna kan binciken maigidan nasa ne a ofishin ‘yan sanda, aka aiko shi ya karɓi wayoyin.

Mai shagon ya gane mutumin a matsayin wanda suka fita tare da ubangidansa, ya fito da wayoyin Muhammad ​​guda biyu ya miƙa wa CID na bogi. Shi ko ɓarawo yaga ya mallaki wayoyin sata guda uku a hannunsa, sai ya arce.

A ofishin ’yan sanda kuwa, har kusan ƙarfe 3 na rana babu labarin CID da ya ce zai je ya dawo. Muhammad ya gaji, sai ya fara yin tambayoyi kamar haka ”ta yaya za a kama ni laifin da ban yi ba”,?
Abin da ban san komai game da shi ba?’

”Aikina shi ne cajin waya, babu ruwana da matsalar mallakin waya. Ina ganin ya kamata a yi cikakken bincike”.

Sulaiman Garba, wanda aka sace ma waya

”Mutumin da ya kawo wayar shagona ya kamata a yi ma tambayoyi, ba ni ba”. Inji Muhammad

‘Yan sandan sun amsa da cewa suna jiran CID ya dawo ne har yanzu. Muhammad ya ba da shawarar su ƙira shi ta waya, suka yi ta ƙira amma ba su samunsa, lambar bogi ce. Haka dai aka ci gaba da jira har ƙarfe biyar na yamma, a lokacin ne dangin Muhammad suka yanke shawarar ziyartar ‘yan sanda domin jin ba’asi.

Sun koka da yadda mutane ke jiran Muhammad a shagon domin karɓar wayoyinsu, don haka akwai buƙatar ‘yan sanda su sake shi. Sannan kuma sun yi tambaya game da inda CID yake, amma ‘yan sanda sun kasa yi musu cikakken bayani.

’Yan’uwan Muhammad ​​sun nuna rashin jin daɗinsu da jami’an da kawai suka yarda da wani labari daga wani baƙo ba tare da wata hujja ko shaida ba saboda ya zo da mari a hannun sa, da katin shaidar ƙarya.

Daga nan ne hankali ya fara tashi. ASP Musa Nuhu ya umarci Sajan da jami’an sa, da su je su nemo wannan CID ɗin a duk inda yake. Bayan sun shafe sa’o’i suna bincike, sai suka sanar da ɓacewarsa. ASP ya shaidawa Muhammad ​​cewa ”tare muka ganku, don haka babu abin da za mu iya yi”.

Ngelzarma chaji Ofis

Aka sallami muhammad, ya kai maganar wajen Lawani, inda Lawanin ya yi alƙawarin taimaka wa Muhammad. Sai dai abin takaicin shi ne, Lawanin bakinsu ɗaya da jami’an tsaro, don haka ya ƙira su, suka tabbatar da faruwar lamarin. Yayin da ya ke ƙiran ‘yan sanda, wasu ma’aurata da ke wurin kan batun aure sun ji shi a lokacin da ya ƙira ‘yan sanda.

Muhammad ​​ya ji ba a neme shi ba har an kwana, sai ya koma. Lawanin ya ce har yanzu bai gana da jami’an ba, don haka ya ƙara haƙuri. Muhammad ya koka da cewa mai wayar, mai suna Sulaiman Garba ya matsa masa sai ya biya shi wayarsa. “Na yi masa bayani cewa wayar tana wurin ‘yan sanda, amma yaƙi yarda da bayanina.”

Lawanin ya yi alƙawarin sasanta lamarin washegari. A washegarin, Lawanin Ya gana da ’yan sanda a cikin wani taron sirri, yayin da Muhammad ​​ke zaune a gindin wata bishiya a waje. Bayan sun tattauna ne suka yanke shawarar cewa Muhammad ​​ya kawo kuɗi su yi amfani da su wajen gano wayoyi ukun da aka sace.

Yanzu dai Muhammad yana cikin wani hali, ga ɓatan wayoyinsa, ga ɓatan wayar kwastomansa, a dalilin sakacin ’yan sanda.

Jaridar Neptune Prime ta ƙira PPRO na Damaturu, Dungus AbdulKareem don jin ta bakinsa, sai yace bai san komai ba game da lamarin. Bayan mun masa bayani, ya nuna rashin jin daɗin faruwar hakan, kuma ya umarce mu da mu bawa su Muhammad lambarsa nan take, domin ya taimaka musu.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba mu san yadda ta ƙare ba tsakanin waɗanda abin ya shafa, PPRO, da kuma sashin ‘yan sanda na Ngelzarma.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Yadda ɗan damfara ya yaudari ’yan sandan Ngelzarma, da wasu mutane biyu: Labarin Bello Muhammad ​​da Sulaiman Garba - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Published

on

'Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da 'yar maƙocinsa

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Daga Shafaatu Dauda,Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta kama wani matashi mai suna Zakariyya Muhammad, da ake zargi da laifin yin garkuwa da ƙaramar yarinya mai shekaru biyu da rabi.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya aike wa da manema labarai a ranar Talata.

Sanarwar ta ce, tun a Ranar 4 ga watan Yuli 2024, rundunar ta samu ƙorafi daga wani Mazaunin unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka, cewar wani ya ƙira wayar sa inda ya shaida masa cewar ya yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Amina , har aka nemi a biya shi kuɗin fansa naira miliyan biyu kafin ya sake ta.

Bayan samun korafin ne Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya tayar da dakarun ‘yan sanda ma su yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin SP Aliyu Muhammad Auwal, tare da ba Su umarnin kuɓutar da yarinyar cikin a wanni 24, da kuma kama waɗanda ake zargin.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ƙara da cewa, an yi nasarar kama wanda ake zargin Zakariya Muhammad , a ranar 5 ga watan Yuni 2024, inda ya tabbatar da cewar shi ne ya yi garkuwa da yarinyar sannan ya nemi kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Kano sun ceto ’yar shekara 2 da maƙocinsu ya sace

Neptune Prime Hausa ta kawo rahotan na cewa tuni aka kuɓutar da yarinyar kuma likitoci sun tabbatar da cewar kalau ta ke.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan Kano, ya ce an dawo da batun babban sashin binciken manyan laifuka dake Bomapai, ɓangaren da ya shafi garkuwa da mutane, kuma da zarar an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Rundunar ta ja hankalin iyaye su dinga kula da ‘ya’yansu, tare da jan kunnen matasa cewar wannan ba abin yi ba ne, kuma ba sana’a ba ce, musamman a jihar Kano domun ma su yunƙurin aikata ba su da wajen ɓuya.

Continue Reading

'Yansanda

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Published

on

An ja hankalin 'yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ja hankalin ‘yan ƙasar game da shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi a faɗin ƙasar musamman a jami’o’i da manyan makarantu.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar Ribas Grace Iringe-Koko ce ta yi wannan jan hankali a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar da maraice a birnin Fatakwal.

Ta bayyana cewa wata babbar ƙungiyar asiri ta Najeriya tana shirin gudanar da gagarumin biki ranar Lahadi a faɗin Najeriya, musamman a jami’o’i don tunawa da mutumin da ya kafa ta.

“Rundunar ‘yan sandan Jihar Ribas ta samu bayanai game da bikin da ƙungiyar Neo-Black Movement (NBM) za ta yi a faɗin ƙasar ranar 7 ga watan Yulin 2024. Ƙungiyar, wadda ake yi wa laƙabi da Aiye ko Black Axe, tana shirin gudanar da bikin ne domin tunawa da wanda ya kafa ta.

KU KUMA KARANTA: Shugaban hukumar leƙen asirin sojin Isra’ila ya yi murabus saboda harin Hamas na 7 ga Oktoba      

Bikin, wanda aka sanya wa suna Ranar AIYE ko 7/7 za a gudanar da shi ne a dukkan jihohin da ke faɗin ƙasa, musamman a manyan makarantu,” in ji sanarwar.

An gargaɗi masu ta da hankalin jama’a a Bikin Dodanni na Egungun a Jihar Oyo

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana sane da munanan ayyukan ƙungiyar asirin na kisan mutane a manyan makarantu da faɗace-faɗace a tsakanin ƙungiyoyin asiri da tayar da zaune-tsaye da sauran manyan laifuka.

Ta ce yanzu haka ta baza ƙarin jami’an ‘yan sanda zuwa wasu wurare domin daƙile ayyukan ƙungiyoyin asiri, sannan ta yi ƙira ga iyaye su gargaɗi ‘ya’yansu su guji shiga ayyukan ƙungiyoyin asiri.

“Ana bai wa manyan makarantu shawarar ƙara matakan tsaro da kuma sanya idanu sosai domin tabbatar da tsaron dukkan ɗalibai.

Kazalika ana ƙira ga dukkan makarantu su lura da duk wani taro na ɗalibai da bai kwanta musu a rai ba,” a cewar sanarwar.

Continue Reading

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like