Rasuwa
Yadda mutuwar Alhaji Mala na shirin ‘Daɗin Kowa’ ta jijjiga Kannywood
A halin yanzu dai masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood a Arewacin Najeriya na cikin jimamin rashin ɗaya daga cikin ma’abotanta.
Allah ya yi wa Aminu Mahmud rasuwa, wanda aka fi sani da Kawu Mala saboda rawar da ya taka a cikin shirin nan na gidan talabijin mai suna ‘Daɗin Kowa,’ wanda ake haskawa a tashar Arewa24.
Jarumin ya yi fama da ciwon zuciya da ya daɗe da ita, a ranar Lahadi da daddare Allah ya masa rasuwa. Alhaji Mala ya kwashe sama da shekaru ashirin yana sana’a, Mala ya samu karɓuwa sosai ta yadda ya taka rawar gani a cikin shirin Daɗin Kowa.
Mala ya rasu, ya bar matarsa ɗaya da ‘ya’ya sama da 10.
KU KUMA KARANTA: Tinubu ya aike da ta’aziyar mutuwar uban ƙasa, dattijo Musa Musawa
A safiyar ranar Litinin ne aka yi jana’izarsa a maƙabartar Haye da ke ƙaramar hukumar Nasarawa a Jihar Kano, kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Murtala Karabiti, ɗaya daga cikin takwarorinsa na riƙo, ya bayyana matuƙar alhininsa game da rasuwar Mala, yana mai bayyana ta a matsayin rashi da ba za a iya maye gurbinsa da shi ba da ya bar wani gagarumin gurbi a harkar.
Karabiti ya ƙara jaddada matsayin Mala da irin jajircewarsa na ci gaban harkar fim a Arewacin Najeriya.
“Likita,” kamar yadda ’yan uwansa suka ƙira Mala da farin ciki, a duk duniya ana ɗaukarsa a matsayin aboki da ɗan’uwa.
Da yake ya san shi fiye da shekaru 20, Karabiti ya ba da shaida na kyawawan halin da Mala yake da shi, yana mai cewa bai taɓa jin wani mummunan labari game da shi ba.
Karabiti ya ƙara da cewa a yayin da masana’antar ke juyayin rasuwarsa, ya zama wajibi a gare mu da mu yi addu’ar Allah ya jikansa.
Ƙasashen Waje
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
Daga Ibraheem El-Tafseer
Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.
A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.
A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.
KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki
Rasuwa
Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa
Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa
Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti bayan gajeruwar rashin lafiya.
Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.
Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.
Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.
KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa
Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.
Rasuwa
Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa
Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa
Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.
Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.
Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.
Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.
KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa
Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: Yadda mutuwar Alhaji Mala na shirin ‘Daɗin Kowa’ ta jijjiga Kannywood - LEGEND FM DAURA
Pingback: Da gaske ne auren jaruma Wasila Isma’il da Al-Amin Ciroma ya mutu? | Neptune Prime Hausa
Pingback: Jarumin Kannywood, Karkuzu ya makance, yana kukan neman taimako | Neptune Prime Hausa
Pingback: Jarumin Kannywood, Karkuzu ya makance, yana kukan neman taimako - LEGEND FM DAURA