Gwamnatin tarayyara ta ba da umarnin rufe iyakokin ƙasa domin zaɓe

3
419

Gwamnatin Tarayya  ta ba da umarnin rufe dukkan iyakokin ƙasar gaba ɗaya gabanin zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya na ranar Asabar.

Kwanturola Janar na NIS, Isah Jere ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Mista Tony Akuneme ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

Jere ya ce za a rufe dukkan iyakokin kasa yadda ya kamata daga karfe 12 na dare ranar Asabar zuwa karfe 12 na dare ranar Lahadi 26 ga Fabrairu.

Don haka, duk masu kula da kwamitocin musamman na jihohin kan iyaka su tabbatar da aiwatar da wannan umarni sosai,” inji shi.

3 COMMENTS

Leave a Reply