Connect with us

Labarai

Ƴan sandan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar mutane a titin Abuja-Kaduna

Published

on

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce ta kama mutanen da ake zargin su da kitsa tare da yawan sace mutane a kan Titin Abuja zuwa Kaduna.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai a Kaduna yayin holen mutanen a hedikwatar rundunar ta Jihar Kaduna, jami’in hulɗa da jama’a Muyiwa Adejobi ya ce cikin wadanda aka kama har da waɗanda ake zargi da kashe ɗaliban Jami’ar Greenfield ta Kadunan.

Ya ce daga cikinsu har da wani “riƙaƙƙen ɗan ta’adda” Ibrahim Abdullahi wanda aka fi sani da Mande, da ake zargin shi ne ya kitsa tare da jan ragamar sace ɗaliban Jami’ar Greenfiled da kashe wasun su, da kuma jagorantar yawan satar mutane da ake yi a kan Titin Abuja-Kaduna.

Mista Muyiwa ya ce an kama Mande ne bayan samun wasu sahihan bayanai da aka yi a Rido Junction na ƙaramar hukumar Chikun a kan hanyar Abuja zuwa Kadunan.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta samu tallafin dala biliyan 1.3 Don ƙarasa hanyar jirgin ƙasa daga Kano zuwa Nijar

Jami’in ya ce mutumin ya amsa cewa shi ne shugaban wani gungu da ke tayar da hankalin mutane a kan Titin Abuja-Kaduna, kuma an sanya shi a jerin riƙaƙƙun ƴan bindiga irin su Dogo Gide da Bello Turji.

Rundunar ‘yan sandan ta ce an kama bindigogi kirar AK-47 guda 48 a yayin da aka kama Mandi kuma ana ci gaba da kokarin gano masu ɗaukar nauyinsa da kuma masu ba shi makamai.

A ranar 20 ga watan Afrilun 2021 ne aka sace daliban jami’ar Greenfield 20 da malamansu biyu, kwana uku bayan nan kuma aka gano gawar takwas daga ciki, yayin da aka saki sauran mutum 14 din ranar 29 ga watan Mayun 2021, bayan sun shafe wata guda a hannun ‘yan bindigar.

Kazalika kakakin ƴan sandan ya bayyana cewa jami’an tsaron sun kuma kama wani riƙaƙƙen shugaban ƴan bindigar wanda ya kitsa harin da aka kai Cocin Saint Raphael a Fadan Kamantan a watan Satumban 2023.

Rundunar ƴan sandan ta kuma bayyana yadda ta kama wani mutum Shedrack John da ake zarginsa da taimaka wa masu satar mutane da abin da ya shafi kula da lafiyarsu a cikin daji.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ya tabbatar da cewa, Sufeto Janar Kayode Egbetokun yana ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen tabbatar da doka da oda, da tabbatar da tsaro da tsaron dukkan ‘yan kasa, da kuma yaki da miyagun ayyuka a faɗin ƙasar.

“Wadannan nasarorin da aka samu a hanyar Abuja zuwa Kaduna a baya-bayan nan na nuna kishin rundunar wajen cika aikinmu na kare rayuka da dukiyoyi. Za a gudanar da irin wannan aikin na musamman a sauran manyan titunan kasar ta hanyar kafa runduna ta musamman da za ta saka ido,” in ji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like