Connect with us

Labarai

Ƙarin kuɗin wutar lantarki a Najeriya, ya bar baya da ƙura

Published

on

Ƙarin kuɗin da Gwamnatin ta ce ta yi kan wutar lantarki ya jawo wani ruɗani wanda ya sa Hukumar Kula da samar da Wutar Lantarki ta Najeriya wato NERC ta ci kamfanin rarraba wutar lantarki ta Abuja tarar Naira miliyan 200 saboda gazawa wajen bin ƙa’idojin da ta gindaya.
Ƙarin ya nuna cewa masu sayan wuta kilowat ɗaya kan Naira 68 yanzu za su saye shi kan Naira 225, kuma wannan ƙari ne da ya shafi masu samun wutar lantarki har na tsawon sa’o’i 20 a kowace rana, kuma irin waɗannan sune aka sa su a kaso na ɗaya, waɗanda ake kira Band A a turance, sannan akwai masu kaso na biyu da ake ce masu Band B da na uku har ma da na huɗu.

Ministan Watsa Labarai Mohammed Idris Malagi ya yi ƙarin haske cewa an yi ƙari ne kan waɗanda ake ganin za su iya, wanda ya zama abu na gwaji.

Idris ya ce waɗannan kuɗaɗen da ake zaton za a samu daga hanun kashi 15 cikin 100 na masu samun wuta na sa’o’i 20 a kowace rana ake so a samu kuɗin tallafi da zai sa a ba sauran ‘yan ƙasa waɗanda suka kai kashi 60 wuta su ma su mora.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Najeriya ta ƙara kuɗin lantarki

Kan batun azarɓaɓi da hukumar ba da wuta ta birnin tarayya Abuja wato AEDC ta yi na sayar da wuta kan sabon farashi kuma, Ministan Watsa labarai Mohammed Idris ya ce an ɗauki mataki na mayar wa wanda aka karɓi kuɗin sa kan kuskure da wuta da zai sha har na tsawon lokacin da kuɗin sa za su ƙare, sannan hukumar NERC ta ci tarar kamfanin AEDC tarar Naira miliyan 200.

Idris ya ce Gwamnati tana iyakacin ƙoƙarin ta saboda tana kashe Naira triliyan 2.9 duk shekara wajen samar wa ƙasa da wutar lantarki.

Amma ga Shugaban Cibiyar kare haƙƙin masu amfani da wutar lantarki a Najeriya Kola Olubiyo, ya ce yawan lalacewar hanyoyin wuta a ƙasar ya sa ‘yan ƙasa suna shan wahala, saboda haka yana ƙira ga shugaban ƙasa da ya soke sayar da hanun jarin da aka yi baki ɗaya, saboda a sake tsari da zai samar wa ƙasa da wutar lantarki na dindindin.

Shi ma Shugaban Marasa Rinjaye a Majalisar Wakilai Kingsley Chinda ya fitar da sanarwa inda ya ce da shi da ‘yan’uwansa ba su amince da ƙarin kuɗin wutar ba kuma zai aike wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da wasiƙar neman a soke ƙarin baki ɗaya sai abubuwa sun daidaita a ƙasa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like