Connect with us

Labarai

Zulum ya ƙaddamar da rukunin gidaje 100 na na gwamnatin tarayya a Gwoza

Published

on

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, a ranar Laraba ya ƙaddamar da wasu gidaje 100 da gwamnatin tarayya ta gina a ƙaramar hukumar Gwoza.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya ruwaito cewa Gwamnatin Tarayya ce ta gina aikin a ƙarƙashin shirinta na ci gaba mai ɗorewa, SDGs.

Gwamna Zulum, wanda mataimakinsa, Usman Kadafur ya wakilta a wajen bikin ya yaba wa manufar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari na ganin ‘yan Najeriya masu ƙaramin ƙarfi sun samu gidaje masu inganci da rahusa.

Ya yi nuni da cewa, ayyukan samar da gidaje za su magance matsalolin ƙarancin gidaje da kuma inganta ayyukan sake tsugunar da al’ummar jihar da tashe-tashen hankula suka yi wa ɓarna.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Zulum ya sake buɗe kasuwar shanu ta Gamboru

A nata jawabin, babbar mataimakiya ta musamman ga shugaban ƙasa kan harkokin SDG, Adejoke Adefulire, ta ce an tsara aikin ne domin tallafawa tsarin ci gaban jihar Borno na BoSDF na tsawon shekaru 25.

Hakan a cewar ta, an yi shi ne da nufin aza harsashi mai inganci da samar da ci gaba mai ɗorewa a jihar. Misis Adefuilire ta ce gidajen an yi su ne domin mutanen da rikicin Boko Haram ya shafa.

“A shekarar 2030, kashi 70 cikin 100 na al’ummar Borno za su tsunduma cikin harkokin rayuwa, tun daga makaranta da kuma aiki kuma wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin tallafawa irin waɗannan shirye-shiryen”, in ji Misis Adefulire.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Zulum ya ƙaddamar da gidaje 200 a Nganzai LG | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Zulum ya ƙaddamar da gidaje 200 a Nganzai LG - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: An rantsar da Zulum, ya godewa al’ummar jihar Borno da suka sake zaɓensa a karo na biyu | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like