Connect with us

Zaɓen 2023

Zamu yi maganin duk wanda ya fito da makami komai girmansa- DIG ga ‘yan siyasa

Published

on

Daga Shafaatu Dauda, Kano

Mataimakin babban sufeton ‘yan sandan Nijeriya DIG Hafiz Muhammad Inuwa da ke kula da harkokin zaɓen shekarar 2023 ayankin jahohin arewa maso yammacin Nijeriya , ya gargadi ‘yan siyasa da magoya bayan su, dasu kaucewa yin wani abu da zai tada hankulan masu zaɓe.

DIG Hafiz M. Inuwa ya bayyana cewa babban sufeton ‘yan sanda na ƙasa IGP Usman Alkali Baba ya umarce su, da su gargaɗi ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki da su jawa magoya bayan su kunne gabanin zaɓen da ke tafe a ranar Asabar 18 ga watan Maris 2023.

DIG Hafiz M. Inuwa ya bayyana hakanne a jahar Kano ,a ci gaba da shirye-shiryen da rundunar ‘yan sanda ta ƙasa ke yi na tabbatar da tsaro da kare rayukan al’umma da kuma dukiyoyinsu .

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda dubu 18,748 aka jibge a Kano saboda zaɓen Gwamna

Ya ƙara da cewa fatan su, shi ne a yi zaɓe lafiya a kammala lafiya, ba tare da nuna siyasa da gaba ba.

‘’duk wani ɗan siyasa indai yana son ci gaban Kano , to zaman lafiya shi ne ci gaban, so ake a zauna lafiya.

‘’kuma na zo da jawabi, in gargaɗe su, Wallahi ba zamu yi ƙasa a gwiwa ba wajen maganin duk wani da ya nemi ya tada fitina, saboda haka ina tabbatar muku da cewa duk wanda ya nemi ya ɗau makami ko dan ya hana wani fito wa zaɓe kodan ya jikkata wani to ‘wallahi tallahi fushin hukuma ne a tattare dashi”. In ji DIG Hafiz.

Ya ce ba zasu raga wa kowa ba duk girmansa kowaye , domin ci gaban Najeriya da ci gaban Kano da kuma zaman lafiya shi ne agaba.

‘’In kunne yaji jiki ya tsira , wanda kuma ya ke ganin zai yi wani abu akasin haka to ga fili ga mai doki’l”

Tun kafin wannan lokacin ne kakakin rundunar ‘yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyana cewa sun tanadi dakarun ‘yan sanda masu yawa dan tabbatar da tsaro a zaɓen ranar 18 ga watan Maris 2023.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: DSS tayi gargaɗi ga ‘yan siyasar da ke shirin yin zanga zanga a ofishinta | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kotu

Kotu ta soke zaɓen Gwamna Lawan na Zamfara

Published

on

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta a ranar Alhamis ta soke nasarar Da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal na jam’iyyar PDP ya samu.

A sakamakon haka, kotun ta bayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba.

Kotun dai ta ce za a sake zaɓen ne a wasu ƙananan hukumomin Jihar guda uku.

Ƙananan Hukumomin su ne Maradun da Birnin-Magaji da kuma Bukyun.

A cewar kotun, hukuncin da Kotun sauraron ƙararrakin zaɓen Gwamnan ya yi a baya, wanda ya tabbatar da nasarar Dauda, bai yi la’akari da hujjar da jam’iyyar APC mai ƙara ta gabatar ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Lawan ya amince da naira biliyan huɗu don gyara hanyoyi a Gusau

Kazalika, kotun ta yi fatali da sakamakon da APC da kuma Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) ta bayar a ƙaramar Hukumar Maradun.

Tsohon Gwamnan Jihar, kuma ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Muhammad Matawalle ne dai ya shigar da ƙarar yana neman a soke nasarar Dauda a zaɓen.

Hukumar INEC dai ta bayyana Dauda Lawal na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen na ranar 18 ga watan Maris din da ya gabata.

Continue Reading

INEC

INEC ta bayyana Uzodinma a matsayin wanda ya lashe zaɓen Imo

Published

on

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana Gwamna Hope Uzodinma na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Imo da aka gudanar a jiya Asabar.

Abayomi Sunday ,jami’in hukumar zaɓe ta INEC daga cibiyar tattara sakamakon zaɓen jihar dake Owerri, ne ya bayyana wanda ya lashe zaɓen a safiyar yau Lahadi.

Hope Odidika Uzodinma ɗan takarar APC ya samu ƙuri’u 540,308 inda ya kayar da abokin hamayyarsa na jam’iyyar PDP, Samuel Anyanwu, wanda ya samu ƙuri’u 71,503 yayin da ɗan takarar jam’iyyar Labour, Athan Achonu, ya zo na uku da ƙuri’u 64,081.

KU KUMA KARANTA: Matasa a Imo sun kama ɗan sanda bisa zargin sace ƙuri’un zaɓe

Hukumar zaɓen Najeriya ganin cewa Hope Odidika Uzodinma ya cika dukkan ka’idojin a ɓangaren da ya shafi doka,banda haka ya kuma samu rinjayen ƙuri’un da suka dace, an ayyana shi a matsayin wanda aka zaɓa.

Continue Reading

Labarai

Matasa a Imo sun kama ɗan sanda bisa zargin sace ƙuri’un zaɓe

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce za ta gudanar da bincike kan zargin tafka maguɗi a zaɓen da aka yi wa ɗaya daga cikin jami’anta a jihar Imo.

Bidiyon wani jami’in da wasu matasa ke riƙe da shi da suka zarge shi da sace ƙuri’a a cibiyar tattara ƙuri’u ta Amakohia Ikeduru a lokacin zaɓen gwamna da aka yi a ranar 11 ga watan Nuwamba.

Da yake mayar da martani ga faifan bidiyon, kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce;

‘’Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta na sane da zargin da ake yi wa wannan ɗan sanda da ake zargin yana da hannu wajen sace ƙuri’u a cibiyar tattara ƙuri’u ta Amakohia Ikeduru da ke jihar Imo. 

KU KUMA KARANTA: ’Yan daba sun buɗe wa masu zaɓe wuta a Bayelsa

Ba mu ɗauki wannan batu da wasa ba domin yana damun sahihancin rundunar da kuma yadda mambobinta za su iya tabbatar da ingancin zaɓe. 

Don haka muna tabbatar wa jama’a cewa za a gudanar da cikakken bincike, kuma za mu yi muku bayani nan da nan.  Yana buƙatar cikakken bincike.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like