’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 ɗauke da ƙoƙon kai a jihar Ogun

0
50
’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 ɗauke ƙoƙon kai a jihar Ogun

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 ɗauke da ƙoƙon kai a jihar Ogun

Daga Muhammad Kukuri

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 da ake zargin matsafi ne ɗauke ƙoƙon kan mutum a garin Abeoluta na Jihar Ogun

Ana zargin mutumin yana shirin yin tsafi da ƙoƙon kan ne a lokacin da ’yan sanda suka kama shi.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sandan Kenya 400 sun tafi Haiti don aikin wanzar da zaman lafiya

Kakakin ’yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta ce jami’an rundunar sun kama wanda ake zargin ne bayan da ya haka wani kabari ya sare kan gawar da ke ciki domin yin tsafi a garin Abeokua.

Odutola ta sanar a ranar Talata cewa rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.

Leave a Reply