Connect with us

'Yansanda

‘Yan sanda sun ƙwato naira miliyan 262 daga masu garkuwa da mutane cikin shekaru uku

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ƙwato kuɗaɗen mutanen da aka yi garkuwa da su kimanin naira miliyan 262 da dubu ɗari 6 tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021.

Bisa ga takardar tantance hatsarurruka na ƙasa na shekarar 2022 da wakilinmu, ya samu daga shafin yanar gizon hukumar kula da harkokin kuɗin ta Najeriya, ta ce, a cikin shekaru uku da suka gabata ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta gudanar da bincike mai nasaba da garkuwa da mutane 28.

Takardar ta yi nuni da cewa, a shekarar 2019, hukumar DSS ta gudanar da bincike-bincike guda 11 da suka shafi garkuwa da mutane, an gudanar da bincike 7 ne kawai a cikin shekarar 2020 da 10 a cikin 2021.

KU KUMA KARANTA:‘Yan sandan Gombe sun kama wasu matasa 4 bisa zargin yin garkuwa

Takardar ta karanto wani ɓangare cewa, “Wannan ya nuna karara cewa, idan aka kwatanta da shekarar 2019, an samu raguwar kashi 36% na adadin wadanda aka bincika a shekarar 2020, kuma idan aka kwatanta da shekarar 2020, an samu ƙaruwar kashi 30 cikin 100 na adadin wadanda aka bincika a shekarar 2021.”

Akan kuɗaɗen da ‘yan sandan suka ƙwato na garkuwa da mutane, takardar ta ce, “ ,’Yan sandan Najeriya sun kwato kuɗi N262, 600,000 kwatankwacin dalar Amurka 635,850 a cikin lokacin da ake bitar kuɗaɗen da aka samu daga satar mutane daga waɗanda suka aikata laifin.

Rahoton ya kara da cewa, “ Laifukan da aka tsara a cikin ƙasa da ƙasa a Najeriya na da matukar tasiri. Ƙungiyar boko haram da ISWAP da ƙungiyoyin ‘yan bindiga da sauran ƙungiyoyin masu garkuwa da mutane da ba a bayyana sunayensu ba a fafin ƙasar nan, suna yin garkuwa da mutane da yawa domin biyan kuɗin fansa, yayin da ƙungiyar asiri ta Black Ax Confraternity da aka fi sani da Neo-Black Movement ke da hannu wajen safarar mutane, safarar muggan ƙwayoyi, damfara da zamba cikin aminci da sauransu”.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, masu garkuwa da mutane na gujewa amfani da cibiyoyin kuɗi da bankuna wajen karɓar kuɗin fansa.

Rahoton ya ce, “Masu garkuwa da mutane suna gujewa biyan kuɗin fansa ta hanyar cibiyoyin kuɗi; ko bankuna, maimakon haka, suna karɓar kuɗin,ta hanyar karɓa da kansu a hannu da hannu ko kuma su yi amfani da wasu kamfanoni, musamman ma’aikatan ofishin ‘yan chanji.”

Rahoton ya ci gaba da cewa, masu aikata laifin na iya kasancewa a shirye suke ko kuma ba a shirye ba, kuma sau da yawa yana haifar da wasu laifuka kamar fataucin mutane, don cire sassan jikinsu.

Haka zalika rahoton ya ce masu aikata laifin na amfani da sassan da dama da kuma hanyoyin ɓoye kuɗaɗe a kan iyakokin kasashen waje, da bankunan kasashen waje.

Rahotanni sun nuna cewa an yi garkuwa da akalla mutane 9,264 cikin shekaru uku.

Kungiyar Enact Africa, wata kungiya ce da ke gina ƙwarewa don inganta martanin Afirka game da aikata laifuka, ta ruwaito ofishin Majalisar ɗinkin ɗuniya kan miyagun kwayoyi da laifuffuka, na cewa an yi garkuwa da mutane 1,386 a shekarar 2019 da 2,860 a shekarar 2020.

Bayanai da aka samu daga hukumar kula da hatsarin harkar tsaro ta Najeriya, wanda Beacon Consulting, sanannen kamfani ne mai kula da haɗarin tsaro da kamfanin tuntubar bayanan sirri ya wallafa, ya nuna cewa an yi garkuwa da mutane akalla 5,018 a shekarar 2021.

A wani rahoto na baya-bayan nan da jaridar The PUNCH ta fitar, wani ƙwararre kan harkokin tsaro kuma tsohon darakta a ma’aikatar harkokin wajen kasar, Mike Ejiofor, ya bayyana cewa, samar da ‘yan sandan jihohi da kananan hukumomi da kuma daukar fasahar zamani zai taimaka wajen rage matsalar rashin tsaro.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Mutum 3 da suka yi yunƙurin kashe ɗan sanda sun shiga hannu | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like