Connect with us

Labarai

’Yan Kannywood da dama sun ƙaurace wa taron da Hisbah ta gayyata a Kano

Published

on

’Yan Kannywood da dama musamman ma fitattun jarumai da daraktoci da furudososhi sun sa kafa sun shure gayyatar da Hukumar Hisbah ta yi musu domin tattaunawa da su a jiya Litinin.

Wakiliyarmu ta ruwaito cewa, ’yan masana’antar fina-finan ƙalilan da ba su wuce 30 ba ne suka halarci amsa goron gayyatar.

Tun dai a ranar Jumaar da ta gabata ne Hukumar ta Hisbah ta bakin Mataimakin Babban Kwamandanta kan Ayyuka, Dokta Mujahideen Aminudden ta bayar da sanarwar cewa za ta tattauna da ’yan fim ɗin ne don yin gyara ga ayyukansu a ci gaba da ayyukan da Hisbar ke yi na ‘Operation Kawar da Badala.’

Sai dai Shugaban ƙungiyar jarumai ta Kannywood Alasan Kwalle ya bayyana rashin jin daɗinsu game da gayyatar ta Hisbah wanda ya ce kamata ya yi ta aika musu takardar gayyata a hukumance.

“Bai kamata Hisbah ta kira mu ta kafar rediyo ba wanda ya yi kama da neman masu laifi. Ko a baya mun zauna da Hisbah wanda kuma mun fa’idantu da tattaunawar.

KU KUMA KARANTA: Yau Hisbah za ta yi zama da ’yan Kannywood

“A yanzu ma za mu halarci zaman matukar dai Hisbar ta gyara kuskurenta.”

Sai dai Babban Kwamandar Hisbar, Sheikh Aminu Daurawa ya ce sun aike wa ’yan fim din takardar gayyata ta hannun Shugaban Hukumar tace Fina-finai da ɗab’i ta jihar Kano, Abba Almustapha.

“Mun sanar ta rediyo ne kawai don amfanin alumma amma ba wai gayyatarsu muka yi a rediyo ba,” in ji Daurawa.

Da yake jawabi a wajen taron, Shaikh Daurawa ya bayyana cewa Hisbar ta damu game da yadda baƙin ƙananan ’yan mata ke kwararowa jihar da sunan shiga fim inda suka yi sansani a wurare daban-daban suna aikata baɗala.

“Ba mu so mu kai musu sumame don haka muke so ku shiga cikin lamarin don yi wa tufkar hanci.”

Daurawa ya ƙara da cewa Hukumar tana son ’yan fim ɗin su gyara wasu kura-kurai da suke yi a fina-finai musamman yanayin sanya tufafi da mummunan lafazi wanda zai iya ɓata tarbiyyar al’umma.

“Mun lura ba wai kawai jarumai ne ke taka rawa a fina-finai ba domin a lokuta da dama jaruman kan yi ƙorafi cewa duk abin da suke a fim darakta da forudusa ne suke sanya su don haka muka haɗa da su a cikin gayyatarmu don mu sami fahimtar juna.”

A jawabinsa, jarumi Abdullahi Amdaz (Excellency) ya bayyana cewa suna sane da irin abubuwan da ke faruwa na assha a masana’antar, wanda kuma ya ce a shirye suke su gyara kurakuransu.

A yayin zaman, an ƙaddamar da kwamitin haɗin gwiwa tsakanin ɓangarorin biyu don laluɓo hanyoyin da za a kawo gyara a harkokin masana’antar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like