Connect with us

INEC

‘Yan IPOB sun bankawa ofishin INEC wuta, suka yi garkuwa da ma’aikata a Imo

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan kungiyar Biafra ta IPOB ne ko kuma ESN sun kona ofishin Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ke ƙaramar hukumar Orlu ta Jihar Imo, inda suka yi garkuwa da wasu ma’aikatan gine-gine. wadanda aka ceto daga baya.

Festus Okoye, kwamishinan hukumar ta INEC na ƙasa kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a, ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Juma’a.

Kwamishiniyar zabe ta jihar Imo, Farfesa Sylvia Uchenna Agu, ta ce an kai wa ofishinmu da ke karamar hukumar Orlu hari, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis 1 ga Disamba 2022.

“Ɓangaren sa, wanda ake kan gyare-gyarensa bayan harin da aka kai a baya, maharan sun lalata shi kuma suka ƙone wani bangare na ginin, sannan suka sace uku daga cikin ma’aikata bakwai da ke aikin gyaran, kafin daga baya suka sake,” inji Okoye.

KU KUMA KARANTA:Zaɓen 2023: An tsaurara matakan tsaro a ofisoshin INEC

Ya ce ɓarnar da ta fi haka,ba dan jami’an ‘yan sandan da suka yi gaggawar tura mutanensu zuwa wurin.

Wannan dai shi ne karo na huɗu da aka kai wa ofishin INEC hari cikin makonni uku da suka gabata.

A kwanakin baya ne aka ƙona ofisoshin INEC a Osun, Ogun, da Ebonyi, tare da lalata dubban katunan zabe na dindindin (PVCs), akwatunan zabe da sauran kayayyakin zabe.

“Wannan hari ya shafi wuri dayawa inda hukumar ta sake bayyana damuwarta kan yawaitar hare-haren da akan cibiyoyinta da kuma illar hakan akan shirye-shiryen zaben 2023” Okoye ya kara da cewa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: A karo na biyu ‘yan bindiga sun kai hari kotun Imo, sun ƙona takardu | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

INEC

INEC ta dakatar da wani jami’inta don gudanar da bincike kan ɓacewar takardun kaɗa ƙuri’a

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta dakatar da wani jami’inta mai suna Mr Fred Ogboji, wanda ke kula da ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, bisa zargin ɓacewar wasu muhimman kayayyakin gudanar da zabe.

Hukumar INEC, a wata sanarwa ta ce ta dakatar da jami’in nata ne don samun sukunin gudanar da bincike a kan ɓacewar takardun kaɗa ƙuri’a na kujerar majalisar wakilai na shiyyar Bassa da Jos ta Arewa a rumfuna goma sha shida, a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

Jami’a a sashen yaɗa labarai na hukumar INEC, Zainab Aminu, ta tabbatar da dakatar da jami’in, don yin bincike.

Duk da umurnin sake yin zaɓen a ranar Lahadi a wasu rumfuna, jami’an zaɓe ba su fito a kan lokaci ba, yayin da a wasu rumfunan jama’a ba su fito don sake gudanar da zaɓen ba.

KU KUMA KARANTA:Ministan Wajen Turkiyya ya yi gargaɗi  kan yiwuwar ɓarkewar rikici, saboda harin da Amurka ke kai wa ƙungiyoyin da Iran ke goyon baya

Mr. Raphael Madugu, wani ɗan jarida a jihar Filato, ya ce sun yi ta ƙoƙarin samun jami’in hukumar zaɓen don ya yi bayani kan matsalolin da aka fuskanta a rumfunan zaɓen amma bai amsa ƙira da saƙonni da aka aike masa ba.

An gudanar da zaɓen Sanata na shiyyar Arewacin jihar Filato da na majalisar wakilai na Jos ta Arewa da Bassa ne bayan da kotu ta soke waɗanda aka zaɓa a ƙarƙashin jami’iyyar PDP, bayan da ta ce jami’iyyar ba ta da zaɓaɓɓun shugabanni a jihar Filato a lokacin da aka gudanar da zaɓukan gama gari a shekara ta dubu biyu da ashirin da uku.

Continue Reading

INEC

Yau ce ranar zaɓen cike gurbi da raba gardama a jihohi 26 na Najeriya

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

An hana zirga-zirgar ababen hawa har zuwa shida na yamma a jihohin da za a yi zaɓen.

A yau Asabar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke gudanar da zaɓukan raba-gardama da kuma na cike giɓi na kujerun majalisun tarayya da kuma na jihohi a 26 a ƙasar.

Za a gudanar da zaɓukan ne a ƙananan hukumomi 80 a faɗin Najeriya, domin cike gurbin wasu da suka rasu da ’yan majalisar da kotu ta cire ko kuma waɗanda suka sauka domin karɓar wasu muƙaman.

A cewar Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, za a yi zaɓen cike gurbi ne a jihohi tara daga cikin 26 domin zaɓar sanatoci biyu da ’yan majalisar wakilai na tarayya huɗu da kuma kujeru uku na majalisar jiha.

A zaɓukan gaba-ɗaya za a yi na kujerun sanatoci uku da kujerun majalisar wakilai 17 da kujeru 28 na majalisun jihohi a faɗin ƙananan hukumomi 80.

Wasu daga cikin fitattun kujerun da za a yi zaɓen nasu su ne, kujerar Honarabul Femi Gbajabiamila, wanda ya yi murabus ya karɓi mukamin Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban ƙasa, da ta Sanata David da Sanata Ibrahim Geidam da Honarabul Bumi Tunji-ojo da Honarabul Tanko Sununu da suka yi murabus domin karɓar muƙamin ministoci.

Akwai kuma kujerar majalisar wakilai ta Honarabul Isma’ila Maihanchi, daga Taraba, wanda ya rasu tun kafin rantsar da shi da kuma Honarabul Abdulƙadir Danbuga daga Sokoto wanda ya rasu a watan Oktoba na 2023.

KU KUMA KARANTA:Babban jami’in MƊD ya damu da yiwuwar kai farmakin da Isra’ila ke yi a Rafah

Jihohin da za a yi zaɓukan sun haɗa da Ebonyi, da Yobe, da Kebbi, da Legas, da Ondo, da Taraba, da Benuwe, da Borno, da Kaduna, da Filato, da Akwa Ibom, da Anambara, da Kuros Riba, da Delta, da Enugu, da Jigawa, da Katsina, da Adamawa, da Bauchi, da Bayelsa, da Kano, da Nasarawa, da Neja, da Oyo, da Sokoto, da kuma Zamfara.

Dangane da zaɓukan Babban Sufeton ‘Yan-sanda Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin hana zirga-zirgar ababen hawa daga ƙarfe 12 na dare zuwa shida na yamma a jihohin da za a yi zaɓen.

Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da al’umma na rundunar ’yan sandan Najeriya, Olumuyi Adejobi ya fitar tun a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ce dokar taƙaita zirga-zirgar ba ta shafi masu muhimman ayyuka ba, kamar ma’aikatan kashe gobara da ‘yan jarida da jami’an INEC da likitoci da masu sanya ido a zaɓukan.

Continue Reading

INEC

INEC ta cire PDP a jerin jami’iyyun da za su shiga zaɓe a Filato

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, ta cire jami’iyyar PDP a jerin jami’iyyun da za su shiga zaɓen da za ta gudanar na ‘yan majalisun tarayya a shiyyar Arewacin jahar Filato.

Gudanar da zaɓen ya biyo bayan shara’ar da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke, inda ta cire sanata mai wakiltar Filato ta Arewa, Simon Mwadkon da ɗan majalisa mai wakiltar Bassa da Jos ta Arewa, a Majalisar wakilai, Musa Agah, bisa hujjan cewa jami’iyyar PDP ba ta da shugabanni kafin gudanar da zaɓen na 2023.

Mataimakin kakakin jami’iyyar PDP a jahar Filato, Alhaji Abdullahi Garba Mai Rake yace tun suna jin ƙishin-ƙishin har dai ya tabbata ba sunan jami’iyyar su a cikin zaɓen na ranar Asabar.

KU KUMA KARANTA: Gamayyar ƙungiyoyin farar hula ta Najeriya ta ɗorawa hukumomi alhakin rashin tsaro

Shugaban ƙungiyar gamayyan jami’iyyu ta IPAC a jahar Filato, Abubakar Dogara yace ba su da hurumin canza matakin da hukumar zaɓen ta ɗauka, sai dai jama’a su yi haƙuri su gudanar da zaɓen cikin lumana.

Mai fashin baƙi kan lamura kuma shugaban ƙungiya mai zaman kanta ta CLEEN, Gad Shamaki Peter ya ce kotu ce kaɗai za ta ƙwato wa PDP ‘yancin ta.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa ta ce zaɓen na ranar Asabar zai cike guraben sanatoci uku, da wakilan Majalisar tarayya goma sha bakwai, da ‘yan majalisun dokoki jaha guda ashirin da takwas a ƙananan hukumomi tamanin a jihohi ashirin da shida na Najeriya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like