Connect with us

Labarai

Yadda za ka kare shafinka na Facebook da Twitter daga masu ƙwace

Published

on

Matakan da mutane yakamata su ɗauka domin kare kansu daga masu yin kutse a shafukan sada zumunta (Hackers).

A wannan lokacin mutane da dama suna fuskantar matsaloli game da yadda ake yi musu kutse a akawun ɗin su irin su facebook, twitter, Instagram da sauransu. Wasu sunanan suna bibiyar yadda za su yi su mallaki wasu bayananka domin su yi maka kutse.

To akwai hanyoyi da dama da za ku iya amfani da su wajen kare kanku daga masu son yi muku kutse. Ga wasu daga cikin hanyoyi biyar da za kuyi amfani da su ku kare kanku kamar haka;

  1. Da farko ka da ku yarda ku saka lambar wayarku ko sunan garin ku ko sunan ƙauyen ku kaɗai a matsayin “Password” a Facebook ko Instagram ko Twitter.
  2. Ka da mutum ya saka “Password” da wani abu da ya shafi bayanansa na shafin facebook.

Misali: Suna na Maryam sai na saka password ɗina a matsayin “MARYAM” ko “MARYAM123” da makamancin wannan.

KU KUMA KARANTA: Anya Facebook dandalin sada zumunta ne kuwa? (I)

  1. Mutum ya saka ” Password” mai wahalar gaske da ya haɗa abubuwa da yawa kamar: Harufa (Alphabets) Babban baƙi (A – Z) da Ƙaramin baƙi (a – z) da Lambobi (0 – 9) da  Symbols (@,#,$,%,-,?,*,£,=) da sauransu. Misali: “Il0v3U_100%@Masoyiyata” = (I Love you 100% Masoyiyata) da sauransu.
  2. Mutum ya yi activating ɗin “Two-factor authentication (2FA)”. Wanda zai taimaka ta yadda babu wanda zai shiga account ɗin ka ko da ya san password da username ɗin ka dole sai yana da “2FA Code” din da aka tura a lambar wayar da aka yi amfani da “Two-factor authentication (2FA)” da shi ko kuma ta cikin manhajar (Authy ko Google Authenticator) da aka seta da shi kafin a iya buɗewa.
  3. Abu na ƙarshe shi ne; a yi activating ɗin “LOGIN ALERT” wanda zai sanar da ku duk lokacin da aka yi ƙoƙarin buɗe shafinku na Facebook da na Instagram da na Twitter ɗin ku. Za’a turo muku da saƙo da cewar “wani mai waya kaza da kaza daga waje kaza ya yi ƙoƙarin buɗe account ɗin ku, shin da izininku ne?” daga nan ko kuce kune ko kuce baku ba ya danganta ga abin da kuke son ku yi a lokacin.

Waɗannan sune kaɗan daga cikin hanyoyi da zamu iya kawo muku su a wannan rubutun da za su taimaka muku wajen kare akawun ɗin ku daga faɗawa hannun masu yin kutse wato Hackers.

5 Comments

5 Comments

  1. Pingback: Manhajar ‘Threads’ da yadda ake amfani da ita | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Zan sauya wa Twitter sabon tambari – Elon Musk | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Yadda za ka kare kanka daga masu ƙwacen Whatsapp | Neptune Prime Hausa

  4. Pingback: Yadda ake amfani da ‘Google Drive’ | Neptune Prime Hausa

  5. Pingback: Yadda ake amfani da ‘Google Drive’ - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like