Connect with us

Al'ajabi

Yadda tsaka ta kashe mutum 6 ‘yan gida ɗaya

Published

on

An gano gawarwakin mutum shida, ‘yan uwan juna da sanyin safiyar Juma’a da ake zargin tsaka ce ta sanya guba a abincinsu.

Waɗanda suka mutun, sun hada da Mista Adeleke John Samuel, mai shekaru 55, da matarsa, Mrs Pamela Adeleke, mai shekaru 50, da ‘ya’yansu biyu da wasu ‘yan uwansu su biyu.

Wata majiya da ta shaida cewa, an gano faruwar lamarin ne, lokacin da mai gadin gidansu, Mista Lawal Ojo, ya ankare da wani irin shiru da tsakar rana, abun da ba a saba gani ba.

Mai gadin ya sanar da maƙwabta waɗanda suka kutsa cikin gidan sai kawai suka ga gawarwakin mutanen a cikin gidan a dakuna daban-daban.

Dukkansu suna cikin yanayin barci, inji majiyar, wanda ke nuni da cewa watakila sun mutu ne a cikin barcinsu.

A cewar wata shaidar gani da ido, Misis Ifenatuora Ijeoma, mai yiwuwa sun ci gubar ne a lokacin liyafar cin abincin da dare.

Ta sake nanata cewa, bayan da aka duba kayan dafa abinci, an gano wata matacciyar tsaka a cikin tukunyar miya da daya daga cikin makwabtan suka yi, don haka suka yi imanin cewa dangin sun mutu ne daga gubar na tsakar.

Tsaka, a kimiyance aka sani da Hemidactylus frenatus, ƙaramar ƙadangare ce mai santsi, mai laushin fata, ta fito ne daga Kudu maso Gabashin Asiya, amma yanzu ana samunta a duk faɗin duniya.

Tsawon tsaka na kaiwa 15cm, kuma yawanci launin toka ne ko launin ruwan kasa mai haske zuwa launin ruwan hoda.

Yawancin lokaci ana danganta tsaka da gubar abinci mai kisa.

KU KUMA KARANTA:Kano Pillars na jimamin mutuwar tsohon ɗan wasanta ƙofarmata

A cewar wani likita wanda kawai ya bayyana kansa a matsayin Dokta Omotosho, masanin ilimin halitta, “Tsaka galibi ba su da illa, sai dai tana ɗauke da kwayoyin cuta da dama a bakinta, waɗanda ke haifar da babbar illa idan mutane suka ci ko suka sha a ruwa.

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘yan sanda sun shiga cikin lamarin, duk da dai har yanzu ana hasashen tushen mutuwar iyalan su shi da.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like