Connect with us

Labarai

Yadda ƙarancin naira ya haddasa rikici a Ogun

Published

on

Tsoro ya dabaibaye mazauna garin Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, da ‘yan kasuwa, yayin da wasu fusatattun matasa suka gudanar da zanga-zanga a sassa da dama na babban birnin jihar.

Rahotanni sun ce an fara zanga-zangar ne a yankin Asero a Abeokuta, a ranar talata, da wasu abokan hulɗar bankin GTBank suka yi kan rashin samun sabbin takardun kuɗi na Naira daga bankin.

Masu zanga-zangar da suka yi tashe-tashen hankula a kan tituna sun tare hanyar da ta nufi Adatan da Osiele zuwa Ibadan a yayin zanga-zangar.

Haka kuma zanga-zangar ta bazu zuwa Adatan, Sapon, Oke-Ilewo, Lafenwa da dai sauransu, inda jama’a suka yi ta rataye ganye a jikin ababan hawansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Lanre Bankole, ya yi gaggawar garzayawa wurin da lamarin ya faru domin kwantar da hankulan da ya tilastawa jami’an bankin dakatar da ayyukansu.

KU KUMA KARANTA: CBN zai hukunta duk bankunan da ke ɓoye sabbin kuɗi

An kuma ɗauki matakin ne a lokaci guda yayin da wasu matasa da suka fusata suka je Sapon, Lafenwa, Adatan, Gbonagun Obantoko inda suka gudanar da zanga-zangar.

Wani banki a Sapon ya dakatar da aikinsa ba tare da bata lokaci ba don gudun kada a kai masa hari yayin da bankunan Oke-Ilewo da Panseke suma suka rufe ofisoshinsu kafin fusatattun matasan su far musu.

An ga wasu ma’aikatan bankunan a Oke-Ilewo da Panseke sun fice daga harabar da gudu, daga bisani matasan sun isa Oke-Ilewo inda suka lalata duk wasu kayan ‘yan siyasa da suka rataya akan fitilun kan titi.

Matasan da ke tafiya a kan babura sun kuma tare hanyar Lalubu a yayin zanga-zangar, inda suka hana zirga-zirgar ababen hawa, sun yi ta harbe-harbe a wasu wurare yayin da ba a ga ’yan sanda ba sai bayan fusatattun matasan sun bar wurin.

Haka kuma wasu masu zanga-zangar sun kai farmaki wani reshen bankin First Bank da ke Lafenwa a Abeokuta inda suka lalata na’urar tantance motoci da ke bankin.

An kuma bayyana cewa an rufe makarantu sakamakon ruɗanin da aka samu yayin da aka kai hari wata makarantar sakandare dake Gbonagun, Obantoko.

Wani malami a makarantar da ya nemi a sakaya sunansa ya ce an jefa barkonon tsohuwa cikin harabar makarantar, kuma malaman sun yi gaggawar kwashe daliban zuwa wuri mafi aminci.

Tarzomar ta garin Abeokuta tayi salwantar mutuwar mutum guda, wanda bidiyonsa yayi ta kareɗe shafin sada zumunta inda aka ganshi an harve shi da bindiga ya riqe wajen a gefen cikinsa a lokacin da yake qoqarin tsallaka kwata amma ya faɗa cikinta.

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like