Connect with us

Al'ajabi

Yadda mace ta yanke azzakarin mijinta, ta kashe shi har lahira

Published

on

Wata mata mai suna Florencia Amado Cattaneo ta yanke azzakrin mijinta tare da daɓa masa wuƙa lamarin da yayi sanadiyar mutuwarsa.

An tsinci gawar mijin matar Pedro Federico Zarate mawaƙi da ya shahara da waƙoƙin aure da bushebushe a yankin Altos de San Lorenzo na ƙasar Ajantina.

Matar mai shekaru 41 da haihuwa, ‘yan sanda sun kama ta da laifin kisan gilla da ake zargin ta da aikatawa, kuma an tura ta ga likitoci don auna lafiyar kwakwalwarta, a cewar kafar yaɗa labarai ta internet ta Mail Online.

KU KUMA KARANTA:Yadda wani mutum ya kashe matar sa saboda burodi

Baya ga yanke al’aurar mijinta, ta kuma bar wata wuƙa binne a cikin kwayar idonsa.

An samu mamacin da wuƙar da matarsa ta caka masa a ido bayan ta yanke masa al’aura.

An kama wanda ake zargin wacce masaniya ce na ilimin halayyar dan adam, a ranar 11 ga watan Janairun 2023 bayan ta gudu zuwa gidan mahaifiyarta a cikin motar haya hannunta yayi ceɓe-cabe da jini, kamar yadda ‘yar uwarta Patricia ta shaida wa kafafen yaɗa labarai.

Ƙanwar matar ta tsinci gawar mijin a kan gado a gidan da suke zaune tare da matarsa ​​da ɗansa ɗan shekara biyar.

An tarar da raunuka daban-daban a jikin gawar, ciki har da kirjinsa, an kuma yanke masa al’aurar kamar yadda kafafen yada labarai na kasar suka ruwaito.

An kwantar da wacce ake zargin a sashin kula da masu taɓin hankali na wata cibiyar kula da lafiya da ke La Plata, inda za a yi mata gwaje-gwaje.

Wanda aka kashe ya kasance mai shirya waka, ya kuma yi aiki a cibiyar al’adun lardin Estacion a La Plata tun 2006. Dan asalin Cordoba, ya auri matar da ake zargi da kashe shi a shekarar 2017.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Yadda uba ya kori ɗansa don ya ziyarci mahaifiyarsa | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Yadda uba ya kori ɗansa don ya ziyarci mahaifiyarsa - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: Ban taɓa azzakarin mai gidan da nake haya ba – Matar da ake zargi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like