Connect with us

Al'ajabi

Yadda kaka ta cinna wa ɗanta, matar shi da jikokin ta wuta a Ondo

Published

on

Wata kaka mai suna lforiti ta bankawa ɗanta da matar da jikoki biyu wuta a unguwar Apomu dake Akure babban birnin jihar Ondo.

Majiyoyi sun ce kakar da ke zaune tare da ɗanta a gida ɗaya ta koka da cewa suna hana ta abinci.

An tattaro cewa ta ƙona gidan a lokacin da ‘yan uwa ke barci, inda ta kashe uku daga cikinsu, ciki har da ɗanta, Victor; matar, Racheal, da ɗaya daga cikin jikokin, yayin da ɗayan yaron ke cikin mawuyacin hali a cibiyar kula da lafiya ta tarayya FMC, Owo.

KU KUMA KARANTA: Yadda wani mutum shaƙe budurwarsa saboda cin amana, ya kuma cinna wa kansu wuta

Da yake bayyana lamarin ga manema labarai a Akure, wani ganau mai suna Korede Michael ya ce, “Mun ga gidan yana ci da wuta da misalin karfe 2:00 na safe a karshen mako, sai da muka fasa tagar domin ceto duk wanda ke cikin gidan.

“Matar, danta, Victor Oloro; mata, Rachael; da yara, Toluwani da Blessing, duk suna cikin gidan lokacin da matar ta cinna masa wuta.

Ta samu busassun kuyan itatuwan dabino da kuma dan ɗanta ya ajiye a galan (na janareta) ta baje gidan sannan ta kunna wuta.

“Ni ne mutum na farko da ya fara ganin gobarar kuma na yi tsalle na shiga gidan kafin sauran jama’a su bi ni wajen ceto su.

“Mun samu mota nan take domin kai su asibitin gwamnati da ke Akure. “Lokacin da muka isa Akure (UNIMED annex), likitoci da ma’aikatan jinya sun ki amincewa da majinyatan, inda suka ce ba za su iya kula da su ba saboda yawan konewar da suka yi, kuma suka ba da shawarar cewa mu kai su Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Owo.

“Abin takaici, mun rasa jikan karshe, wanda yake ɗan shekara biyu da rabi kacal, nan take muka isa Owo. “Ɗan da matarsa, suma, sun mutu yayin da jikan ɗaya tilo da ya rage yana cikin wani mawuyacin hali.”

Korede ya ce gobarar ba ta shafe wanda ake zargin ba ko kadan. “Yaran ba za su iya fitar da matar daga gidan ba lokacin da ta fara wani abin ban mamaki, saboda marigayi mijinta ne ya gina shi.”

Majiyar ‘yan sandan ta ce wadda ake zargin ta amsa cewa ta ƙona danta da iyalansa ne saboda yunwar da suke barin ta da shi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Funmi Odunlami, yayin da take tabbatar wa wakilinmu afkuwar lamarin, ta ce yanzu haka lamarin yana hannun sashen binciken manyan laifuka na jihar.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: An yi kira ga hukumar Lantarki ta YEDC ta inganta yadda take ba da wuta a Yobe | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: An yi kira ga hukumar Lantarki ta YEDC ta inganta yadda take ba da wuta a Yobe - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: ‘Yan sanda sun cafke mutumin da ya yi yunƙurin cinnawa masallaci wuta | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like