Connect with us

Labarai

Yadda ɗalibi ya kashe abokinsa bayan ya daɓa masa wuƙa a Bauchi

Published

on

Daga Ahmad SAKA, Bauchi

Jami’an ‘yan sandan jihar Bauchi, sun kama wani matashi mai suna Kamaluddeen Musa mai shekaru 22, ɗalibi a kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa da ke karamar hukumar Kangere-Bauchi bisa laifin kashe abokinsa kuma ɗalibin makarantar sabida saɓani.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan SP Ahmed Mohammed Wakil ya bayyana hakan ga manema labarai a Bauchi.

Ya ce, “A ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 da misalin karfe ɗaya na rana, bayanan da rundunar ta samu sun nuna cewa a ranar da misalin karfe 9:15 na safe, Kamaluddeen Musa ya daba wa abokinsa Usman Umar wuƙa, mai shekaru 25 , a cikinsa”

KU KUMA KARANTA:Yadda amarya ta kashe kishiyarta akan tsire

Wakil ya ce lokacin da ‘yan sandan suka isa wurin; sun ɗauki wanda aka daɓa wuƙan, zuwa Asibitin ƙwararru na Bauchi, inda likitoci suka tabbatar da cewa ya mutu, yayin da nan take aka kama wanda ake zargin.

Ya ce, “Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wadanda ake zargin da wanda aka kashen abokanai ne kuma ɗaliban makarantar sakandare ta Adamu Tafawa Balewa College of Education Kangere, Bauchi LGA, Jihar Bauchi.

“Kuma a ranar 28 ga Nuwamba, 2022 da misalin karfe 09:15, an samu ‘yar hatsaniya a tsakanin su, a lokacin da marigayin ya yi kukan cewa wanda ake zargin ya fita ba tare da sanar da marigayin ba, lamarin da ya haifar da fada wanda ya yi sanadin rauni a yatsar wanda ake zargin, ana cikin haka sai wanda ake zargin ya zaro wata karamar wuka daga aljihunsa ya daɓa wa marigayin, a cikinsa.

KU KALLI BIDIYON ANAN:https://fb.watch/h8EhyaqX_A/

“Shaidun sun tabbatar da hakan; Musa Danjuma mai shekaru 22 da Nawasi Sadi mai shekaru 20, dukkansu daliban makaranta ne da suka shaida lamarin”

Kakakin ‘yan sandan ya ce har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike kamar dai yadda aka yi a lokacin da aka bada labarin, domin gano ƙarin bayanai bayanan.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Wani matashi da ya kashe budurwarsa don ya saci motarta ya shiga hannu | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like