Connect with us

Labarai

Wani uba da aka kashe ɗansa na neman adalci, ya koka kan diyyar naira dubu 600 da aka ba shi

Published

on

Danjuma, mahaifin Mohammed Danjuma da aka kashe, ya koka yana neman a yi masa adalci, kan kisan gillar da aka yi wa ɗansa.

An yi zargin kashe Mohammed mai shekaru 34, wanda ya kammala karatun digiri na biyu a makarantar horar da ma’aikatan jiragen ruwa ta Nigerian Maritime Academy da ke Oron, a ranar 7 ga watan Yulin 2022, a unguwar da ke titin Clapperton, a jihar Sakkwato.

Mahaifin marigayin, Danjuma Sidi, wanda ya ba da labarin irin halin da ‘yan uwa ke ciki, ya bayyana wa manema labarai cewa, ana zargin ana shirin yin maƙarƙashiya da bincike inda ya gurfanar da waɗanda ake zargin a kotu da kisan dansa.

Ya ce rundunar ‘yan sandan Sakkwato ba ta bada wani taimako da tayi masu, domin duk ƙoƙarin da suka yi na neman ‘yan sanda game da kisan da ake zargin, hukumar ta PPRO ta yi watsi da su.

KU KUMA KARANTA:Wani matashi da ya kashe budurwarsa don ya saci motarta ya shiga hannu

Da aka tuntubi rundunar ‘yan sandan jihar a ranar larabar da ta gabata, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ASP Abubakar Sanusi, ya yi wa ‘yan jarida alkawarin za su binciki lamarin tare da yi musu bayani.

Cike da hawaye, Ɗanjuma Sidi ,ɗan shekaru sittin da biyu, ya shaidawa manema labarai cewa an kashe Mohammed, a ranar 7 ga Yulin 2022, kuma bayan watanni biyar, waɗanda ake zargin da kashe shi, suna kan titi suna yawo cikin walwala.

“Akwai shaidar bidiyon da ke yawo, inda aka ɗaure ɗana, aka azabtar da shi, aka wulakanta shi,har ya mutu. Daga nan ne ‘yan sanda suka kai farmaki inda aka kama mutane shida.

“A dalilin binciken, dangin waɗanda ake zargin sun tuntuɓe mu, tare da rokon a sasanta lamarin ba tare da an kai ga ‘yan sanda ba. Na ce da su su ƙyale a yi adalci domin babu wani sassan ta da zai dawo min da ɗana. Sun tafi sun yi alƙawarin dawowa gareni.

“Abin takaici, suka dawo bayan sun saba alƙawarin haɗuwar mu har sau biyu, suka ba ni naira dubu ɗari shida kacal, a matsayin diyya na ran ɗana, tare da binne lamarin.

” Wannan, na ƙi karba, domin idan za su ba ni diyya a Musulunci, ba wannan dan ƙaramin kuɗi naira dubu ɗari shida zasu bani ba.

“Ina amfani da wannan dama wajen yin kira ga gwamnatin jihar Sakkwato da ta tarayya, da Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, da ƙungiyoyin kare hakkokin ɗan Adam da ‘yan jarida, da su taimaka wajen ganin an yi adalci ga ran ɗana da aka kashe”. Inji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like