Connect with us

Labarai

Tinubu na neman majalisa ta amince da kuɗin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Tinubu, ya buƙaci majalisar dokokin ƙasar da ta ƙyale shi ya nemo ƙarin fiye da dala miliyan ɗari biyar don samar da tallafi a wani mataki na rage raɗaɗin cire tallafin man fetur.

Cikin wata wasiƙa da ya aike wa majalisar wakilan ƙasar, shugaban ya buƙaci ‘yan majalisar da su yi wa kasafin kuɗin 2022 kwaskwarima don ba shi damar samo kuɗin.

Shugaban majalisar Tajudden Abbas, ya karanta wasiƙar a yayin zaman majalisar na ranar Laraba.

Abin da wasiƙar ta ƙunsa shi ne akwai kuɗin a ƙasa, to amma shugaba Tinubun na fatan majalisar za ta gaggauta amincewa da wannan buƙata ta sa.

Shugaban majalisar ya sanar da cewa za a duba wannan buƙata a ranar Alhamis.

KU KUMA KARANTA: Na zaɓi na cire tallafin man fetur a ranar farko duk da babu shi a jawabina – Tinubu

A shekarar da ta wuce ne tsohon shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya gabatar da batun samar da dala biliyan ɗaya don gudanar da manyan ayyuka a wani ƙwarya-ƙwaryar kasafin kuɗi da ya gabatar.

Dillalan man fetur sun ƙara farashin man fetur da aƙalla dala ɗaya kan kowacce lita a duk sassan Najeriya bayan Tinubun ya sanar da cire tallafin man fetur a yayin jawabin da ya gabatar a ranar da aka rantsar da shi.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Cire tallafin mai: COEASU ta umarci malamansu da su yi aikin kwanaki biyu a mako | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Majalisar Wakilai za ta binciki dalilin ƙaruwar farashin man fetur a Najeriya | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Tinubu ya amince da kafa asusun gina ababen more rayuwa a jihohi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like