Tag: Yan sanda
-
Dalilin bayyanar jami’an tsaro da yawa a Jigawa – ‘Yan Sanda
Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa an ga yawan manyan jami’an tsaro a Jigawa ne domin daƙile rashin zaman lafiya a zaɓen da za a sake gudanarwa a ranar Asabar. A cewar kwamishinan ‘yan sanda, Effiom Ekot, lamarin ba shi da alaƙa da fashewar wani abu da ya faru ranar Talata a Dutse inda mutum…
-
An kori ‘yan sandan dake tsaron Rarara saboda wasa da alburusai
Hukumar ‘yan sandan Najeriya, a ranar Alhamis, ta kori jami’an da ke tsaron fitaccen mawaƙin siyasar nan na jam’iyar APC mai mulki, Dauda Adamu Kahutu Rarara. Olumuyiwa Adejobi, kakakin rundunar ‘yan sandan, wanda ya sanar da matakin a hedikwatar rundunar da ke Abuja, ya ce an kori jami’an ne saboda ɓatar da harsasai babu gaira…
-
‘Yan sanda sun daƙile fashi a Abuja, sun kama wanda ake zargi
A ranar Laraba ne jami’an ‘yan sanda da ke aiki a sashin Apo da ke Abuja, sun daƙile wani harin fashi da makami tare da cafke wani da ake zargi. Kakakin rundunar ‘yan sanda a babban birnin tarayya Abuja, Josephine Adeh, a cikin wata sanarwa da ta fitar, ta ce an gudanar da wannan aika-aika…
-
‘Yan sanda sun kashe ‘yan bindiga biyu a Zamfara
Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta bayyana cewa, rundunar ta ɗauki matakin daƙile wasu ‘yan bindiga guda biyu tare da daƙile wani hari da aka kai wa wasu al’umma a ƙaramar hukumar Tsafe. Wata sanarwa a ranar Litinin a Gusau ta hannun Kakakin Rundunar, CSP Muhammad Shehu, ya ce Kwamishinan ‘yan sandan, Kolo Yusuf ya…
-
‘Yan sanda sun kama jami’an tsaron Rarara saboda harbin iska
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da cafke wani jami’in ‘yan sanda da ke tare da fitaccen mawaƙin siyasar nan na jam’iyyar APC mai mulki, Dauda Kahutu Rarara, kan harbi ba tare da izini ba. A cikin wani faifan bidiyo, an ga wasu ‘yan sandan da ke tare da shi guda biyu suna harbin iska…
-
‘Yan Sanda sun kama ɗan gidan yarin Kuje da ya gudu
Rundunar ‘yan sanda a jihar Nasarawa ta kama Salisu Buhari, ɗaya daga cikin fursunonin gidan gyaran hali na Kuje da ya tsere daga gidan yari a watan Yulin 2022. Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa ɗauke da sa hannun kakakin rundunar ‘Yan Sandan jihar Nasarawa, Ramhan Nansel a ranar Lahadi a Lafiya. Mista…
-
‘Yan bindiga sun kashe mutane 3 a Legas – ‘Yan sanda
Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe mutane uku a Gowon Estate da ke unguwar Ipaja a jihar. Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labarai na Njeriya (NAN) a…
-
‘Yan sanda dubu 18,748 aka jibge a Kano saboda zaɓen Gwamna
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce kimanin jami’an tsaro dubu 18,748 ne aka baza a fadin jihar domin gudanar da zaɓukan gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki na ranar 18 ga watan Maris. Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mamman Dauda ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labara na…
-
Yadda ‘yan sanda suka ceto ɗan jarida daga hannun masu garkuwa da mutane
Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun a ranar 11 ga Maris, 2023, sun ceto wani ɗan jarida mai suna Oduneye Olusegun, wanda wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi a unguwar Mobalufon da ke Ijebu Ode a ranar 9 ga watan Maris, 2023. A wata sanarwa da Abimbola Oyeyemi mai magana da yawun rundunar…
-
Yadda ‘yan sanda suka ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Zamfara
Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta tarwatsa sansanin ‘yan bindiga tare da ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Zamfara. Waɗanda abin ya shafa dai sun shafe kwanaki 68 a hannun masu garkuwa kafin daga bisani ‘yan sanda su kubutar da su. A cewar rahoton da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN),…