Tag: Yan sanda
-
‘Yan sanda sun kama wata mata da ta yanka ‘yar aikinta da wuƙa a Legas
‘Yan sanda a jihar Legas sun kama wata mata ‘yar shekara 30 mai suna Eucharia Ndigwe da ta yi amfani da wuƙa wajen yi wa ‘yar aikinta ‘yar shekara 15 mummunar rauni, sakamakon rashin wanke jaka. Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Benjamin Hundeyin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya ranar Lahadi a Ikeja…
-
‘Yan sanda sun kama matar da ta gudu bayan ta daɓa wa yarinya ‘yar shekara 8 wuƙa
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta cafke wata mata mai suna Fatima Salisu ‘yar shekaru 35 da haihuwa bisa laifin daɓa wa wata yarinya ‘yar shekara 8 da haihuwa wuƙa a ciki. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna-Kiyawa, ya tabbatar da kamun a wata sanarwa da ya raba wa manema…
-
Da wane dalili ‘yan sanda suka lakaɗa wa ɗan Okada duka a Legas?
Wani ɗan Okada, mai suna Alasan Usman matashi mai ƙoƙarin neman na kansa domin rufawa kansa da ‘yan uwansa asiri. A ranar jumu’a ‘yan sanda a jihar Legas suka tare shi suka ce ya kawo babur ɗinsa duk da dai bai san laifin da ya aikata ba, sai ya ƙi ya basu. Saboda ya ƙi…
-
Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ta kama ƙaurayen da suka addabi jama’a da satar wayoyi
Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ta sanar da kama wasu mashahuran mutane 2 da aka fi sani da Ƙauraye, waɗanda suka shiga wani shago tare da sace wayoyin hannu guda 48. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Gambo Isah ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a…
-
‘Yan sanda sun kashe ‘yan ta’adda, sun ceto mata 5 a Katsina
Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta bayyana cewa jami’anta sun kashe wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne tare da kuɓutar da wasu mata biyar da aka yi garkuwa da su a ƙaramar hukumar Dutsinma ta jihar. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Gambo Isah, ne ya bayyana hakan a wata…
-
‘Yan sanda sun cafke mutumin da ya yi yunƙurin cinnawa masallaci wuta
‘Yan sanda sun cafke wani mutum da ya yi yunƙurin cinnawa wani masallaci wuta a birnin Dresden na ƙasar Jamus da yammacin jiya Talata. Mutumin ya zubar da fetur a gaban wani masallaci kuma ya yi ƙoƙarin cinnawa ginin wuta, in ji kakakin ‘yan sandan. Shaidu sun ƙira lambar hukumar bayar da agajin gaggawa bayan…
-
Hukumar kula da aikin ‘yan Sanda ta amince da biyan albashin ma’aikatan 2021/2022
Hukumar kula da aikin ‘yan sanda (PSC) , ta amince da biyan albashin ma’aikatan ‘yan sanda na shekarar 2021/2022 waɗanda suka wuce kwalejojin ‘yan sanda da kuma aikin ‘yan sanda. Ikechukwu Ani, kakakin hukumar ta PSC ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja. Ya ce, waɗanda abin ya…
-
Hukumar ‘yan sanda ba za ta amince da cin zarafin jami’anta ba – Arase
Shugaban hukumar ‘yan sanda, PSC, Solomon Arase, ya nanata cewa ba zai lamunta da rashin ɗa’a da cin zarafin ‘yan sanda a kan jama’a ba. Mista Arase, wanda tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda ne, IGP ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, lokacin da Peter Gad, Babban Daraktan gidauniyar ‘Clean Foundation’ ya…
-
Yobe ta samu sabon kwamishinan ‘yan sanda
CP Garba Ahmad ya zama sabon kwamishinan ‘yan sanda na jihar Yobe. DSP Dungus Abdulkarim, kakakin rundunar ‘yan sandan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Damaturu. Ya ce kwamishinan wanda ya karɓi ragamar mulki daga hannun CP Haruna Garba ya fara aiki a ranar Talata. KU KUMA KARANTA:…
-
‘Yan sanda sun kama Yunusa Ari, kwamishinan zaɓe da aka dakatar a Adamawa
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar da cewa kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa Hudu Yunusa-Ari da aka dakatar yana hannunsu. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Muyiwa Adejobi, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, inda ya ce tawagar ‘yan sanda da tsare-tsare, sa ido da tantance zaɓuka sun kama…