Tag: Jami'a
-
‘Yan bindiga sun kai hari a jami’ar Filato – Jami’a
Jami’ar Jihar Filato, (PLASU), ta ce jami’an tsaronta sun daƙile wani hari da ‘yan bindiga suka kai harabar jami’ar a daren ranar Talata. Hukumar makarantar ta ce wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan kwanan ɗaliban makarantar da ke Bokkos tsakanin daren Talata zuwa Laraba amma ba a yi garkuwa da su ba. John Agams,…
-
Jami’ar ATBU ta hana shigar nuna tsaraici ga ɗalibai
Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa dake Bauchi, (ATBU), ta ce daga yanzu za ta ɗauki mataki a kan duk ɗaliban da suka saɓa wa ƙa’idojinta na shigar rashin ɗa’a da tufafi a jami’ar kamar yadda yake ƙunshe a kundin dokokin ɗaliban da aka yi wa kwaskwarima. Dokokin da aka yi wa kwaskwarima na ƙunshe ne a…
-
Jami’ar Najeriya ta yi tayin karɓar dalibai daga Sudan da yaƙi ya hana ci gaba da karatu
Daga Haruna Yusuf Gwamnatin tarayya a ranar Alhamis ta ce wasu jami’o’in ƙasar sun yi tayin karɓar ɗaliban Najeriya da suka dawo daga Sudan da ke fama da rikici. “Mun yi hakan da Ukraine, lokacin da suka dawo, akwai shirye-shiryen ci gaba da karatu a gare su,” in ji shugabar hukumar ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen…
-
Hukumar NSCDC ta tura jami’ai 422 don sanya ido kan UTME a Kano
Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC ko civil defence a jihar Kano, ta tura jami’ai 422 zuwa cibiyoyi 37 da aka ware na jarrabawar shiga manyan jami’o’i, UTME, da ke jihar. Kwamandan jihar, Adamu Salihu, ya bayyana haka a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a Kano ranar Laraba. Ya bayyana cewa…
-
Jami’ar Jihar Yobe ta yi bikin zuwan sabbin ɗalibai 2,740
Mataimakin Shugaban Jami’ar Jihar Yobe dake Damaturu, Farfesa Mala Mohammed Daura, ya bayyana cewa Jami’ar ta kai wani mataki na ɓullo da shirin koyon aikin jinya a Jami’ar, wato ‘B.Sc Nursing’ a Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiyar. Mataimakin shugaban jami’ar ya bayyana hakan ne a yau Laraba 19 ga watan Afrilu 2023 a wajen bikin maraba…
-
An kashe ɗalibin jami’a akan bashin naira dubu ɗaya
Wani sabon ɗalibi da ya kammala digiri a jami’ar Adekunle Ajasin Akungba, Akoko (AAUA), jihar Ondo, mai suna Temitayo, ya yanke jiki ya faɗi a kan bashin N1,000. Rahotanni sun bayyana cewa, an caka wa marigayin wuƙa ne da Almakashi da sanyin safiyar ranar Alhamis, 6 ga watan Afrilu, a kusa da tashar mai na…
-
Yarinyar da ke rubutu da yatsun ƙafa ta sami damar shiga jami’a
Yarinyar nan ‘yar shekara 22 da haihuwa mai suna Maryam Umar wadda aka haifa ba tare da hannu ba, ta roki ‘yan Najeriya masu tausayi da gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu da su kawo mata agaji domin ta kammala rijistar ta zuwa Jami’ar Jihar Gombe. Maryam ta samu gurbin karatu a fannin tattalin arziki…
-
Jami’ar jihar Legas ta hana ɗalibanta sanya tufafin nuna tsaraici
Mataimakiyar shugaban jami’ar jihar Legas (VC), Farfesa Ibiyemi Olatunji-Bello, ta umurci malaman jami’ar da su ɗauki matakin fara hana ɗalibai shiga ɗakunan karatu saboda sanya tufafin da ba su dace ba, masu bayyana tsaraici. Olatunji-Bello, a cikin wata sanarwar ta bayyana cewa wasu ɗalibai sun ci gaba da yin watsi da ka’idojin jami’ar kan ka’idojin…