Connect with us

Labarai

Ta’addanci babbar masifa ce da aka shigo da ita Afirka daga waje – Shugaba Tinubu

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce ta’addanci “babbar masifa ce da aka shigo da ita” kuma ya zama wata annoba ga nahiyar Afirka.

A jawabin da ya gabatar a wajen buɗe wani babban taron yaƙi da ta’addanci na kasashen Afrika na kwanaki biyu a Abuja babban birnin ƙasar, Tinubu ya bayyana cewa ana kashe biliyoyin kuɗaɗe da suka kamata a yi amfani da su wajen kula da lafiya da ilimi da samar da ababen more rayuwa a nahiyar a duk shekara, duk a wajen sayen makaman yaƙi da ‘yan ta’adda.

“Dole ne mu yi magana a kan wannan mummunan bala’i da aka shigo da shi wanda yake son karya mu, mu ga cewa lallai ba mu bari hakan ya faru ba,” in ji shi.

Ya ce, ‘yan ta’adda na neman ƙarfafa son zuciya a nahiyar da kuma kawar da mulkin dimokuraɗiyya da kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali da harkokin tattalin arziki na ƙasashe da dama.

Ya bukaci shugabannin ƙasashen Afirka da su magance talauci da inganta ilimi ba ya ga salon yaƙi da ta’addanci da sojoji ke yi.

Shugaban na Najeriya ya kuma buƙaci takwarorinsa na yankin da su mayar da hankali kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da ake amfani da su wajen samun kuɗaɗen ta’addanci.

“Wadɗanda suke tunanin hakar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba ba ta da wata alaƙa da tallafa wa ta’addanci to sun yi kuskure sosai. Ƙasashen duniya suna da alhakin halin taimakawa a wannan harka saboda da kudaden waje ake hada-hadar ba kudin Afirka ba, wadanda su ke haifar da wadannan miyagun ayyuka,” ya ce.

Mataimakin Sakatare Janar na ofishin yaki da ta’addanci na Majalisar Dinkin Duniya Vladimir Voronkov, ya ce taron na da nufin magance matsalar ta’addanci da ke ƙara ƙamari a nahiyar.

Ya ce ƙungiyoyin ‘yan ta’adda irinsu Daesh/ISIS da Al-Qaida da masu alaƙa da su suna matsawa kudu zuwa mashigin tekun Guinea da ke kudanci da tsakiyar Afirka bayan sun kafu a yankin Sahel, inda ya yi ƙira da a ƙara ba da haɗin kai tsakanin shugabannin nahiyar domin dakile yaduwar ta’addanci.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya buƙaci ‘yan Najeriya su haɗa kansu don ciyar da ƙasar gaba

Shawarwarin Tinubu

Shugaban na Najeriya ya bayar da muhimman shawarwari a wajen taron ƙolin na yaƙi da ta’addanci na ƙasashen Afrika, kamar:

  1. Samar da wata cibiya ta tsakiya ga kasashen Afirka don musayar bayanai da hada kai don yaki da ta’addanci
  2. Magance tushen ta’addanci, tare da talauci da rashin daidaito
  3. Yanke hanyoyin samar da kudade don ta’addanci, kamar haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba da kuma biyan kuɗin fansa
  4. Haɓaka ƙarfi da ingancin ƙungiyoyin da ke yaƙi da ta’addanci
  5. Ƙirƙirar dakaru na musamman don mayar da martani cikin gaggawa game da ta’addanci da sauran barazanar tsaro
  6. Kafa kwamitin da zai haɗa kai da samar da jagoranci kan yaki da ta’addanci
  7. Ƙarfafa ƙarfin yaƙi da ta’addanci na daidaikun ƙasashe
  8. Dakatar da yaɗuwar makamai masu haɗari a faɗin Afirka.
  9. A dauki kwakkwaran mataki don magance barazanar tsaro a nahiyar.

Taron mai taken karfafa haɗin gwiwa tsakanin shiyya da kafa cibiyoyin yaki da ta’addanci a nahiyar Afirka, ya samu halartar mataimakiyar babban sakataren MƊD Amina Mohammed da shugabannin ƙasashe da gwamnatocin ƙasashen Afirka da dama da kuma manyan jami’an MƊD.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like