Connect with us

'Yansanda

Ta sayar da jaririnta ɗan wata 18 a kan kuɗi Naira 600,000 a Ogun – ‘Yan sanda

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Ogun ta tabbatar da cafke wata mata ‘yar shekara 33, bisa zarginta da sayar da jaririnta mai watanni 18 a kan kuɗi Naira dubu 600,000 a yankin Sango-Ota da ke jihar.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa a Sango-Ota a ranar Litinin, ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Abimbola Oyeyemi. “Har yanzu ‘yan sanda ba su gano wanda ake zargin ya sayi jaririn ba.

An kama wanda ake zargin ne biyo bayan ƙorafin da mijin matar, Nureni Rasaq ya shigar a Hedikwatar ‘yan sanda shiyya ta Sango.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in kula da zirga-zirgar ababen hawa a Ogun

“Rasaq, ya ruwaito cewa matarsa ​​ta bar gida zuwa Legas a ranar 15 ga Maris, tare da jaririyarsu amma ta dawo gida ba tare da jaririn ba.

“Ya ce duk kokarin da aka yi na sanin abin da ya faru da jaririn ya ci tura saboda matar ta ka sa bayar da cikakken bayani game da inda jaririn yake,” in ji kakakin ‘yan sandan.

Oyeyemi ya ce bisa wannan ƙorafin, jami’in ‘yan sanda na shiyya ta Sango, CSP Ɗahiru Saleh, ya yi ƙarin bayani ga jami’an da suka gudanar da bincikensa domin bin sawun matar kuma ba tare da ɓata lokaci ba aka kama ta.

Ya ƙara da cewa da ake yi masa tambayoyi, wadda ake zargin ta amsa cewa ta sayar da jaririn ga wani a Legas a kan kuɗi Naira 600,000.

Oyeyemi ta ce da aka tambaye ta dalilin da ya sa ta sayar da jaririnta, wanda ake zargin ya ce ta ci bashin kuɗi ne a wani banki mai ƙaramin ƙarfi, kuma da ta ka sa biyan kuɗin, sai jami’an bankin suka fara yi mata barazana.

“Ta gudu zuwa Legas ta fara sharar ruwan buhu. A cikin aikin ne ta haɗu da wani mutum, wanda ya gabatar da ita ga matar da a ƙarshe ta sayi yaron,” in ji shi.

Muƙaddashin kwamishinan ‘yan sandan jihar, DCP Babakura Muhammed, ya bayar da umarnin a miƙa wanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin ci gaba da bincike da kuma yiwuwar dawo da jaririn.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like