Connect with us

Ƙasashen Waje

Sojojin Nijar sun amince su tattauna da ECOWAS

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Wasu bayanai na nuna cewa sojojin na Nijar a yanzu sun ɗan sassauto inda suka nuna alamun yarda su tattauna da ECOWAS.

A baya sojojin sun ƙi bayar da dama ga wata tawaga ta musamman da ECOWAS ta tura Nijar ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban mulkin soja na Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar domin tattaunawa.

A ranar Asabar majalisar dokokin ƙungiyar ta ƙasashen Afirka ta Yamma ta ce za ta tura wani kwamiti babban birnin Nijar ɗin Niamey.

Sai dai kuma ba ta sanar da ainihin lokacin da za ta tura kwamitin ba.

KU KUMA KARANTA: Ƙasar Rasha ta gargaɗi ƙungiyar ECOWAS game da ɗaukar matakin soji

Haka kuma a ranar Litinin ɗin ne kwamitin tsaro na ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU, kasashe 55 zai gana domin tattauna yanayin na Nijar.

Ana ganin wannan wata alama ce ta nuna damuwa kan wannan juyin mulki, wanda ya kasance na bakwai a tsakanin ƙasashen Afirka ta Yamma da Afirka ta Tsakiya a cikin shekara uku.

Wani abu da ke ɗaukar hankali a kan halin da nahiyar ke ciki dangane da juyin mulkin da ake samu shi ne ba wai makomar Nijar ba kaɗai, wadda kasa ce mai arziƙin sinadarin yureniyom, da kuma kasancewarta kawar ƙasashen Yamma a yaƙi da masu iƙirarin jihadi, akwai fargabar gogayya da ake samu da sauran manyan ƙasashen duniya abokan hammayyar Yamma, domin samun tasiri a nahiyar.

Ƙungiyar Tarayyar Afirka da majalisar Ɗinkin Duniya da kuma Tarayyar Turai dukkaninsu sun mara baya ga ECOWAS a kan duk matakin da za ta ɗauka na mayar da dimukuraɗiyya da kuma Shugaba Bazoum kan mulki.

Ƙungiyoyin har ma da Amurka sun nuna damuwa game da lafiyar shugaban kan halin da aka ce yana ciki, saboda yadda yake tsare.

A ranar Asabar ne wata tawaga ta shugabannin addinin Musulunci ƙarƙashin jagorancin Shaikh Bala Lau, na ƙungiyar Izala ta je Yamai domin tattauna batun na Nijar.

Tawagar wadda ta samu ganawa da sabon Firaministan da sojoji suka naɗa, Ali Mahaman Lamine Zeine, ta kuma samu ganawa da jagoran juyin mulkin wanda ya naɗa kansa sabon shugaban ƙasa Janar Abdourahamen Tchinai.

Bayanai sun nuna cewa tawagar ta shugaban na ƙungiyar Izala ta je Nijar ɗin ne bisa izinin ƙungiyar ECOWAS da kuma shugabanta wanda kuma shi ne shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, domin kwantar da hankali ganin yadda lamarin ke neman haifar da tashin-tashina saboda matakin soji da ECOWAS ke cewa za ta ɗauka.

Ganin yadda matakin da ECOWAS ta ɗauka na sanya wasu jerin takunkumai a kan Nijar ɗin na neman haifar da tsama tsakanin ƙasashen biyu, malaman sun nuna wa sojojin cewa wannan mataki ne na ƙungiya amma ba Najeriya ba, kamar yadda bayanai suka nuna.

A makon da ya gabata ne Sheikh Bala Lau da ‘yan tawagar tasa suka gana da Shugaba Tinubu a Abuja, inda bayanai suka ce a wannan zama ne aka tsara zuwa ganawa da shugabannin juyin mulkin na Nijar.

ECOWAS ta jaddada cewa har yanzu dukkanin wata ƙofa ta sasanta rikicin na Nijar a buɗe take, kuma matakin soji zai ci gaba da kasancewa zaɓi na ƙarshe idan komai ya ci tura.

Ministan harkokin waje na gwamnatin Nijar da sojojin suka hamɓarar, Hassoumi Massaoudou, yace matakin soji da ECOWAS ke cewa za ta ɗauka a kan masu juyin mulkin ba yaƙi ne a kan Nijar da ‘yan ƙasar ba, matakin tabbatar da doka ne a kan waɗanda ya ƙira masu garkuwa da mutane da masu taimaka musu.

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like