Connect with us

Labarai

Sheikh Muhajjadina ya nemi gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki kan tsadar rayuwa

Published

on

A daidai lokacin da al’umma Najeriya ke fama da hauhawar farashin kayyakin abinci da tsadar rayuwa, sanannen malamin addinin nan na Jihar Kano, Sheikh Mujajjadina Sani Kano, wanda kuma shi ne Shugaban Masu Ilimin Taurari na Afirka, ya yi ƙira ga shugabanni a dukkan matakan gwamnati da su gaggauta ɗaukar matakin kawo wa mutane sauƙin matsin rayuwar da suke fuskanta in har suna son kauce wa fushin Allah (SWT).

Sheikh Muhajjadina ya yi wannan bayanin ne a hirarsa da manema labarai a garin Kano ranar Talata. Ya kuma ƙara da cewa, halin da mutaten ke ciki da matsin rayuwa ya wuce duk yadda ake tunani. “Lamarin a halin yanzu ya kai matsayin Innalillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun”.

Ya ce, babu wani ɓangare na rayuwar al’umma da ba su dandan wannan halin da ake ciki. A kan haka malaman addini musulmunci dana addinin Kirista suka haɗu a yin ƙira ga gwamnati ta samar wa al’umma mafita.

Shehin Malamin wanda shi ne kuma shugaban Gidauniyar (Muhajjadina Humanitarian Foundation) wadda ta shahara wajen tallafa wa al’umma, ya ƙara da cewa, a kullum suna samun mutane masu neman taimako maza da mata da marayu masu lalulori daban-daban., “ Yanzu kusan kowa ka gani a hanya yana buƙatar taimako” in ji shi.

Ya kuma ce, mataki mai muhimmanci da ya kamata gwamnati ta ɗauka don kawo ƙarshen matsalar tsadar rayuwa shi ne dawo da tallafin man fetur da wannan gwamnatin ta janye a farkon kama mulkinta. Ya ce, man fetur ya shafi dukkan ɓangarorin rayuwar al’umma, janye shi ya haifar da tsadar rayuwa. Kuma gashi darajar naira na kara karyewa a kullum, “In har gwamnati ta dawo da wadannan abubuwan biyu to da yardar Allah abubuwa za su yi sauki” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: Sheikh Muhajjadina ya yi Allah wadai da harin sojoji kan masu Mauludi a Kaduna

Daga nan Shekih Muhajjadina ya yi gargaɗin cewa, in har gwamnati ba ta ɗauki matakin kawo wa al’umma sauƙin rayuwa ba, to lallai za su gamu da fushin Allah (SWT). “Allah na iya ƙwace mulkin ya ba waɗanda za su taimaka wa mutane” in ji shi.

Ya kuma nemi gwamnati a dukkan mataki su nemi shawarwarin malaman addini wajen gudanar da harkokinsu, musamman abin da ya shafi raba wa al’umma tallafi, “Domin daga cikin malamai ne ake da tabbacin samun masu tsoron Allah, waɗanda za su jagoranci raba wa mutane abin da aka tanada, ya kuma kamata a cire duk wani na’u’i na siyasa a wajen bayar da tallafi, domin yunwa bata san banbanci a tsakanin ‘yan APC ko ‘yan PDP ba” in ji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like