Connect with us

CBN

Saboda masu tara kuɗin haram muka sauya takardun kuɗi, inji Buhari

Published

on

Ba don Talaka muka sauya kuɗi ba, sai don mutnen da suka tara kuɗin haram, inji Buhari

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin ganin an inganta rabon sabbin kuɗaɗen Naira.

A wata sanarwa da Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban ƙasa ya fitar a ranar Asabar, shugaban ya ce an yanke shawarar sake fasalin naira ne domin magance tarnaki na haramtattun kuɗaɗe.

Yayin da yake amsa rahotannin kan dogayen layuka a bankunan, Buhari ya ce babban bankin Najeriya (CBN) yana aiki kan shirye-shiryen “hana hargitsi” kan rabon sabbin takardun kuɗi.

KU KUMA KARANTA:CBN zai hukunta duk bankunan da ke ɓoye sabbin kuɗi

“Shugaban kasa Muhammadu Buhari, a ranar Asabar ya ba da tabbacin cewa gwamnati za ta tabbatar da cewa ‘yan ƙasa basu da wata matsala a harkokin kasuwancin su kuma ba za a samu cikas ba ga dukkanin hanyoyin samar da kayayyaki da suka taso daga musayar kuɗin da zai kawo ƙarshe nan ba da dadewa ba,” in ji sanarwar.

“Da yake mayar da martani kan wasu dogayen layukan da aka yi na jiran mutane na tsawon sa’o’i kafin su iya ajiye tsofaffin takardun kuɗi su samu sababbi, lamarin da ya jawo fushin jama’a da sukar ‘yan adawa, Shugaba Buhari ya sake bayyana cewa an yi canjin kuɗin ne domin mutane da suka tara kuɗaɗen haram ba wai talaka ba. , da kuma cewa ya zama dole a hana jabu, cin hanci da rashawa, da tallafin ‘yan ta’adda.

“Wannan, in ji shi, zai daidaita da kuma ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar.

“Yayin da yake lura da cewa mafi yawan al’umma na fuskantar ƙunci domin sau da yawa sukan ajiye maƙuɗan kuɗaɗe a gida don kashe su, shugaba Buhari ya ba da tabbacin cewa gwamnati ba za ta bar su ga makomarsu ba.

“Ya sake nanata cewa akwai shirye-shirye da dama daga babban bankin kasa da kuma dukkan bankunan kasuwanci don hanzarta rarraba sabbin takardun kuɗi da kuma yin duk abin da ya dace don daƙile taɓarɓarewar kuɗi da hargitsi.”

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Na cika alkawuran da nayi wa ’yan Najeriya a lokacin yaƙin neman zaɓe – Buhari | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

CBN

Ba ƙarancin takardun kuɗi ba ne a ƙasar, yawan tsabar kuɗin dake hannun jama’a muke so a rage – CBN

Published

on

A daidai lokacin da wasu ‘yan Najeriya ke ƙorafe-ƙorafe a kan ƙayyade yawan kuɗin da za su riƙa cira a ATM ko kuma a cikin banki da ake kallo a matsayin yiwuwa akwai ƙarancin takardun kuɗi ne a ƙasar, masu ruwa da tsaki a fannin hada-hadar kuɗi a bankuna sun ce babu matsalar ƙarancin kuɗi.

Sun ce illa dai ana ƙoƙarin ƙarfafa wa ‘yan ƙasa da su riƙa amfani da hanyoyin yanar gizo wato electronic channels wajen samun biyan buƙata ne don rage yawan tsabar kuɗin dake zirga-zirga a cikin ƙasar.

Babban Bankin Najeriya CBN dai ya ce kuɗaɗen da ke zirga-zirga a ƙasar sun kai Naira tiriliyan uku da biliyan 690 a watan Fabrairun da ya gabata wanda shi ne adadi dake zirga-zirga mafi yawa a tarihin ƙasar.

Alƙaluman da suka bayyana haka bayan taron kwamitin manufofin kuɗin bankin wato MPC wanda aka sanar a ranar talata 26 ga watan Maris da muke ciki.

‘Yan Najeriya daga sassa daban daban sun yi ta ƙorafi dai a kan taƙaita adadin kuɗin da za su iya cira a cikin banki ko a ATM kamar yadda wani ɗan ƙasa, Abdulaziz Mala ya ce ya je cire kuɗi kuma dubu 5 kawai ya iya cira.

Saidai wani jigo a bankin Access ya shaida wa Muryar Amurka ta wayar tarho cewa taƙaita iya kuɗin da mai asusu zai iya cira abu ne na bai ɗaya a dukkan bankuna ne kuma wani sashi ba zai iya ƙayyade yawan kuɗin da za’a iya cira ya bambanta da na sauran ba.

KU KUMA KARANTA:Kotu ta umurci CBN ta biya wani Bajamushe naira Miliyan 63 da ta tsare ba bisa ƙa’ida ba

Yana mai cewa mutum zai iya cire Naira dubu 20 sau huɗu a machine ɗaya kuma matakin rage tsabar kuɗin da za’a iya cira ba ya rasa nasaba da ƙoƙarin rage yawan kuɗin dake zirga-zirga a cikin ƙasa wanda ya samo asali tun lokacin sauya launin kuɗi.

A wani ɓangare kuma mai sharhi a kan al’amurran yau da kullum Suleiman Hashim ya bayyana cewa bankin CBN ƙarƙashin Gwamna Olayemi Cardoso ya ɗora a kan dokar nan na rage yawan tsabar kuɗi dake cikin ƙasar ne saboda adadin dake yawo shi ne mafi girma a tarihin ƙasar.

Alƙaluman kididdiga na baya-bayan nan dai sun yi nuni da cewa an sami ƙari a adadin Naira dake zirga-zirga a cikin ƙasar da kaso 1.8 cikin 100 na wata-wata daga Naira tiriliyan 3.65 da aka sanar a watan Janairun shekarar 2024 da muke ciki.

Idan ana iya tunawa tun bayan batun sauya launin kuɗi ake fama da matsalar adadin yawan kuɗi da mutane za su iya cira a cikin asusunsu na banki lamarin da wasu ‘yan kasuwa ke ƙorafe-ƙorafe a kan wanda har yanzu akwai mutane masu ɗimbim yawa da ba sa amfani da hanyoyin yanar gizo wato electronic channels wajen hada-hadar kuɗinsu na yau da kullum.

Continue Reading

CBN

Babban Bankin Najeriya ya ƙara kuɗin ruwa zuwa kashi 22.75 cikin 100

Published

on

A yayin taronsu na farko a wannan shekara, kwamitin Harkokin Kuɗi na Babban Bankin Najeriya ƙarƙashin gwamnan bankin CBN, ya ƙara kuɗin ruwa zuwa kashi 22.75 cikin 100.

A wata sanarwar da CBN ta wallafa a shafinta na kafar X, an sanar da cewa gwamnan bankin Olayemi Cardoso, ya ƙuduri aniyar tsuke bakin hada-hadar kuɗaɗen ruwa, inda ya yi ƙarin awon MPR zuwa kashi 22.75% daga kashi 18.75% cikin 100.

Gwamnan bankin ya sanar da hakan ne ranar Talata bayan taron kwamitin da ya gudana a birnin tarayyar Najeriya, Abuja, inda hedikwatar babban bankin take. An bayyana cewa duka mambobin kwamitin su 12 sun amince da wannan mataki.

A nazarin tattalin arziki, ƙara kuɗin ruwa wani mataki ne da ke da manufar janyo hankalin masu ajiyar kudi a bankuna, don su ƙara yawan kuɗaɗen da suke ajiyewa a asusun ajiya da bankuna ke biyan kuɗin ruwa kan ajiya.

Idan yawan masu ajiye kuɗi a asusun banki ya yawaita, to za a samu raguwar adadin kudi da ke yawo a hannun mutane, wanda yawan shi ne ke zaman daya daga musabbaban da ke kawo raguwar darajar kuɗin ƙasa, da hauhawar farashi.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta umurci CBN ta biya wani Bajamushe naira Miliyan 63 da ta tsare ba bisa ƙa’ida ba

A wani ɓangaren kuma, ƙara kuɗin ruwa yakan rage yawan masu cin bashin banki, wadanda za su ga tsadar cin bashin, musamman idan sun kwatanta da ribar da za su iya samu ta amfanin da kudin bashin don kasuwanci, ko yin wata hada-hadar kuɗi.

Kafin wannan sabon mataki na CBN, yawan kuɗin ruwa da aka ƙayyade a kasar shi ne kashi 18.75, tun bayan taron kwamitin da ya gudana a watan Yuli na shekarar 2023.

Da ma dai alhakin babban bankin ƙasa ne ƙayyade kuɗin ruwa da bankunan da ke ƙasa za su caji masu karɓar bashi, walau kamfanoni, ko gwamnatoci, ko ɗaiɗaikun mutane da ke hada-hadar kuɗi a ƙasar.

Babbar manufar ƙayyade kudin ruwa ita ce sarrafa yawan kudade da ke hannun mutane. Ana ƙoƙarin rage yawan kuɗin da ke yawo a tattalin ariziki don shawo kan hauhawar farashi, ko kuma a ƙara yawansa don haɓaka cinikayya da hada-hadar kuɗi a tattalin arziki.

A zaman kwamitin da Mista Cardoso ya jagoranta, an kuma kara mafi ƙarancin adadin tsabar kuɗin da ake buƙatar bankunan kasuwanci su ajiye a lalitarsu zuwa kashi 45 cikin 100, na kason jimillar adadin kuɗaɗen ajiya da kwastomomin bankin suka zuba a asusun kowane banki.

Haka kuma, an bar adadin ƙarfin iya biyan bashi da bankuna ke da shi a kashi 30 cikin 100, wanda adadi ne da ake aunawa da yawan tsabar kudi da bankuna ke da shi idan an kwatanta da bashin da ake bin su.

Continue Reading

CBN

Ba mu da niyyar mayar da dalolin da ke bankuna zuwa naira – CBN

Published

on

Babban Bankin Najeriya, CBN, ya nesanta kansa daga wani labari da ake yaɗawa kan cewa yana da niyyar mayar da kimanin dala biliyan 30 da ke asusun ajiyar kuɗaɗen waje na bankunan Najeriya zuwa naira.

Babban bankin ya sanar da hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar inda ya musanta lamarin tare da cewa ana yaɗa labarin ne domin saka fargaba a zukatan jama’a.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da nairar ke ci gaba da karyewa a kasuwar hada-hadar ƙasashen waje inda har ta kai ga an canja dala ɗaya kan naira 1,500 a ƴan kwanakin nan.

“Wannan zargin ƙarya ce kuma ana yin sa ne domin saka fargaba a kasuwar hada-hadar ƙasashen waje, wadda CBN ke tuƙuru domin daidaitawa, kamar yadda ayyuka na baya-bayan nan da tsare-tsare suka nuna,” in ji babban bankin.

KU KUMA KARANTA: Amurka ta soke tallafin dala miliyan 442 da take ba wa Nijar

“An yaɗa irin waɗannnan ƙarerayin kan aikin CBN a watannin da suka gabata kuma a bayyane take kan cewa ana so a yi ƙafar ungulu ne ga irin ƙoƙarin da muke yi.

“Muna so mu tabbatar wa jama’a cewa CBN na da aminci kuma ba za ya yi duk wani abu da zai kawo matsala ga kuɗi ko tattalin arziki ba,” in ji babban bankin.

Ko a cikin makon nan sai da aka rufe wasu daga cikin manyan kasuwannin canji na bayan fage da ke Najeriya domin nuna rashin jin daɗi dangane da karyewar darajar nairar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like