Connect with us

Labarai

Rikici a kan tabar wiwi ya yi ajalin mutum ɗaya a Gombe

Published

on

An cafke wasu matasa uku sun kashe wani dilan tabar wiwi saboda saɓanin da ya shiga tsakaninsu da shi kan tabar wiwi a Jihar Gombe.

Rundunar ’yan sandan jihar ta kama matasan ne a Unguwar Gabas da ke garin Deba na Ƙaramar Hukumar Yamaltu, bayan sun yi wa dilan wiwin wannan aika-aikan.

Kakakin rundunar, ASP Mahid Mu’azu Abubakar ya shaida wa manema labarai a yayin da yake holen matasan cewa a ranar 12 ga watan Fabarairu 2024 wani mai suna Mustapha Mato ya kai rahoto ofishin ’yan sanda na garin Deba da cewa faɗa ya kaure a tsakanin waɗannan matasa uku da wani ɗan shekara 30 da suka caka wa wuka ya mutu.

A cewarsa, suna samun wannan rahoto ne jami’ansu suku bazama domin gudanar da bincike, inda suka gano cewa wanda aka kashe ɗin dilan tabar wiwi ne kuma rikici tsakanin sa da kwastomominsa ne ya jawo faɗa har suka soke shi da wuka ya ce ga garinku nan.

KU KUMA KARANTA: An kama ’yar shekara 20 da buhu 5 na tabar wiwi

Ya ce, ’yan sandan na ci gaba da gudanar da binciken kan wadanda aka kama kuma da zarar sun kammala za su tura su zuwa kotu.

An zanta da matasan uku waɗanda suka labarta mata yadda lamarin ya kasance har ta kai ga mutuwar abokin faɗan nasu, inda suka ce fada ne ya hada su bayan ’yan sanda sun kai masa samame ya gudu ya bar tabar wiwinsa.

Matasan da ke hannu sun ce bayan faruwar hakan ce washegari ya yi zargin cewa su ne suka kwashe masa tabar wiwinsa da ya tsere ya bari.

Sun ce, a dalilin haka ne ya tattaro yara da adduna da wukake inda a garin faɗa suka soki ɗaya daga cikinsu, sai su ma suka kwace wukar suka caka wa Sama’ila a baya da kuma wuyansa, wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwarsa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like