Connect with us

Labarai

NEMA ta ba da tallafin kayan agaji ga mutane dubu 23 a Nijar

Published

on

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), ta bayar da tallafin kayayyakin agaji ga manoma da kuma marasa galihu 23,000 da ambaliyar ruwa na shekarar 2022 ta shafa a Nijar.

Babban daraktan hukumar Mustapha Ahmed ne ya bayyana haka a lokacin ƙaddamar da rabon kayayyakin tallafin a Minna ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ba da rahoton cewa an yi wa laƙabi da “Special National Economic and Livelihood Emergency Intervention (SNELEI)”.

Ahmed, wanda Abubakar Yusuf, mai kula da rabon kayayyaki ya wakilta, ya ce an ɗauki matakin ne don tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta shafa a shekarar 2022 da kuma sauran waɗanda suka fi kowa rauni don daƙile illolin bala’in.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NEMA ta ba da sanarwar ambaliyar ruwa ga al’ummomin Adamawa

“Ku tuna cewa abin baƙin ciki na bala’in ambaliyar ruwa na 2022 ya shafi al’ummomi da dama a faɗin ƙasar ciki har da Nijar,” in ji shi.

Malam Ahmed ya lissafa abubuwan da suka haɗa da; injin ɗinki da niƙa, buhunan shinkafa 25, buhunan wake da dawa 10, gishirin mai, buhunan tumatir da kayan yaji.

Sauran sun haɗa da gidajen sauro, tabarmar roba, barguna, bokitin robobi,  katifu, tukwane, sabulun wanka da na wanki da murhun dafa abinci.

Sauran sun haɗa da: masara da irin shinkafa, maganin kashe ƙwari, masu inganta girma, takin ruwa da fanfunan ruwa, da dai sauransu.

Mista Ahmed ya shawarci waɗanda suka amfana da su yi amfani da kayayyakin yadda ya kamata domin inganta zamantakewa da tattalin arziƙinsu.

A nasa jawabin, mataimakin gwamnan Neja, Garba Yakubu, ya yabawa hukumar (NEMA) kan yadda ta kasance a kodayaushe domin ceto waɗanda aka zalunta.

Mista Garba, wanda Bello Ibrahim ya wakilta, mataimakinsa, ya ce kayayyakin za su taimaka sosai wajen ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin gwamnatin jihar na kawo agaji ga waɗanda abin ya shafa.

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Garba Salihu, muƙaddashin darakta janar na hukumar bayar da agajin gaggawa ta Neja (NSEMA), ya yi alƙawarin cewa za a raba kayayyakin ga waɗanda abin ya shafa na gaske.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin, Suleiman Ibrahim, ya godewa gwamnatin tarayya bisa wannan karimcin, inda ya ƙara da cewa kayayyaki za su yi nisa wajen rage musu raɗaɗi.

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like