Connect with us

Labarai

Najeriya za ta ba da lasisin haƙar ma’adinai ga kamfanonin da ke aiki cikin ƙasar

Published

on

Najeriya za ta ba da sabbin lasisin haƙar ma’adinai ne kawai ga kamfanonin da suka gabatar da wani shiri kan yadda za a sarrafa ma’adanai a cikin gida, ƙarƙashin sabbin ƙa’idojin da ake samar da su, kamar yadda kakakin gwamnati ya tabbatar a ranar Alhamis.

Wannan na nuni da cewa an samu sauyi daga tsarin da Najeriya ta kwashe shekaru da dama ta yi na fitar da albarkatun ƙasa zuwa ƙasashen waje yayin da gwamnatocin ƙasashen Afirka ke ɗaukar matakai na fitar da ƙarin ƙimar ma’adinan da suke da shi.

Domin ƙarfafa zuba jari, Najeriya za ta baiwa masu zuba jari ƙwarin guiwa da suka haɗa da hana harajin shigo da kayan aikin haƙar ma’adanai, da sauƙaƙa samun lasin na samar da wutar lantarki, da ba da damar mayar da cikakkiyar ribar da aka samu da kuma inganta tsaro, in ji Segun Tomori, mai magana da yawun ministan bunƙasa ma’adanai na Najeriya.

Tomori ya ce, “Kafin musanya, dole ne mu sake duba shirinsu na kafa masana’antar da kuma yadda za su ƙara wa tattalin arziƙin Najeriya daraja.” Bai bayyana lokacin da za a kammala ƙa’idojin ko kuma za su fara aiki ba.

Sai dai a makon da ya gabata Ministan Ma’adanai Dele Alake, ya ce a yanzu manufar gwamnati ce ta sanya ƙarin darajar ya zama sharaɗin samun lasisi ta yadda za a samar da ayyukan yi da kuma taimakawa al’ummomin yankin.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

Alake, wanda kuma ke jagorantar wata ƙungiyar dabarun haƙar ma’adinai ta Afirka da ta ƙunshi ministocin ma’adinai daga Uganda, Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo, Saliyo, Somalia, Sudan ta Kudu, Botswana, Zambiya da Namibiya, na da ƙudirin yin wani yunƙurin a duk faɗin nahiyar don samun mafi girman fa’ida daga cikin gida daga binciken ma’adinai.

Najeriya, wacce ke kan gaba wajen samar da makamashi a nahiyar Afirka, ta yi ta faman fitar da kimarta daga ɗimbim albarkatun ma’adinai da take da su, sakamakon rashin kuzari da kuma rashin kulawa. Ɓangaren haƙar ma’adinai da ba a ci gaba ba yana ba da gudummawar ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na dukiyoyin cikin gida na ƙasar.

A shekarar da ta gabata Najeriya ta fitar da ma’adinan dala da yawansu ya kai kimanin Naira biliyan 137.59 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 108.34, musamman zuwa ƙasashen China da Malaysia, kamar yadda hukumar ƙididdiga ta ƙasar ta bayyana.

Gwamnati na da burin ƙara zuba jari a fannin ta hanyar ba da wasu lasisi, inda ta kafa wani kamfani mai fa’ida na ma’adinai mallakin gwamnati wanda ke baiwa masu zuba jari kashi 75% na hannun jari tare da kafa wani sashin tsaro na musamman da ke da alhakin yaƙi da masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like