Connect with us

Labarai

Muƙarraban Buhari na yi wa Tinubu zagon ƙasa, inji El-Rufa’i

Published

on

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya bayyana cewa wasu jami’an gwamnatin tarayya a fadar Aso Rock Villa na ƙoƙarin tada zaune tsaye a kan nasarar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, tare da ƙokarin dusashe nasararsa a babban zaɓen da za a yi a watan nan.

El-Rufai ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Laraba.

Ya ce, “Na yi imanin akwai wasu mutane a cikin Villa da ke son mu faɗi zaɓe saboda ba su samu ba; suna da ɗan takararsu, ɗan takararsu bai ci zaɓen fidda gwani ba,” in ji El-Rufai.

A cewar gwamnan Kaduna, waɗanda ke adawa da nasarar Tinubu su ne mutanen da Tinubu ya kayar da ’yan takararsu na shugaban ƙasa a zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar a bara.

El-Rufai ya ce makiyan Tinubu da ake zargin sun boye a ƙarƙashin manufofin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari don daƙile nasarar da tsohon gwamnan jihar Legas ya samu a zaɓen watan nan.

Ya ce, “Suna kokarin ganin mun faɗi zaɓe ne, kuma suna fakewa da burin shugaban ƙasa na yin abin da yake ganin ya dace.

KU KUMA KARANTA:PDP ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wa Shugaba Buhari a Kano, ta ɗora laifin kan Tinubu da Ganduje

“Zan ba da misali guda biyu: wannan tallafin man fetur da ake kashewa ƙasar tiriliyoyin Naira, wani abu ne da muka amince a cire.

“A gaskiya, na yi tattaunawa da shugaban ƙasa na nuna masa dalilin da ya sa ya tafi,domin ta yaya za ku iya samun babban kasafin kuɗi na naira biliyan 200 na titunan tarayya sannan ku kashe naira tiriliyan 2 wajen tallafin man fetur? Wannan tattaunawa ce da na yi da shugaban ƙasa a shekarar 2021 lokacin da abin tallafin ya fara tashi, ya gamsu, mun tafi.

“Kowa a cikin gwamnati ya yarda, kuma ya canza, misali na biyu da zan bayar shine sake fasalin kuɗin.

“Dole ne ku fahimci shugaban,jama’a suna zargin Gwamnan babban bankin ne da laifin sake fasalin kuɗin, amma a’a sai dai ku koma ku kalli ficewar Buhari a matsayin shugaban ƙasa na farko.

“Ya yi wannan; gwamnatin Buhari da Idiagbon sun canza mana kuɗin mu kuma sun yi su a asirce da nufin kamo waɗanda ke wawure kuɗaɗen haram, niyya ce mai kyau.

Shugaban kasa yana da hakkinsa, amma yin hakan a wannan lokaci a cikin lokacin da aka ba shi ba ya da wata, ma’ana ta siyasa ko tattalin arziki.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like