Connect with us

'Yansanda

Mata sun yi zanga zanga kan kisan da ɗan sanda yayi wa lauya a Legas

Published

on

Gamayyar ƙungiyoyin mata sama da 223 ƙarkashin ƙungiyar Womanifesto sun buƙaci a yi adalci kan kisan da da ɗan sanda mai mukamin ASP, Drambi Vandi ya yi wa wata mace lauya mai ɗauke da juna biyu, mai suna Omobolanle Raheem mai shekaru 41, mamba a ƙungiyar lauyoyin Najeriya a Legas.

ASO Darambi Vandi ya harbe lauyar ne a ranar Kirismeti a lokacin da ta ke hanyarta ta dawowa tare da iyalinta, kisan da ya ɗuki hankalin jama’a da dama a faɗin ƙasar nan.

Yayin da suke bayyana amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba a matsayin “barazana ga rayuwa, ‘yanci, tsaro da kariya daidai a karkashin doka”, matan sun ce akwai tsauraran ƙa’idoji na kasa da ƙasa da ke nuni da yadda ‘yan sanda ya kamata suyi amfani da ƙarfi, ko bindigogi.

“Muna buƙatar a gaggauta gurfanar da Drambi Vandi gaban ƙuliya bisa dokar laifuka ta jihar Legas ta shekarar 2015 da sauran dokokin da suka dace.

“Iyali da abokan mamaciyar, Omobolanle Raheem sun cancanci a yi musu adalci da kuma a biya su ga asarar da suka yi da kuma raunin da suka ji” in ji su.

Babbar daraktan Womanifesto na cibiyar bincike da tattalin arziki na mata, Dokta Abiola Akiyode-Afolabi, ta yi tsokaci ne a cikin wata sanarwa mai taken, ‘Adalci ga Omobolanle Raheem da ASP Drambi Vandi ya kashe!’.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Baya ga ƙungiyar mata ta WARDC, sauran waɗanda suka rattaba hannun sun haɗa da Women Lobby Group 100, Women Aid Collective, Women’s Rights Advancement and Protection Alternative, Above Whispers Media Foundation, Dr Oby Ezekwesili, Farfesa Adenike Grange, Moji Makanjuola, Saudatu Mahdi, Josephine Effa-Chukwuma, Esther Eghobami , Farfesa Ayodele Atsenuwa, Bisi Fayemi, Farfesa Yinka Omorogbe, Julie Oyegun da Josephine Anienih.

Sauran sun haɗa da Farfesa Funmi Para-Mallam, Ene Obi, Fame Foundation, Ebere Ifendu, Christian Women for Excellence and Empowerment in Nigeria Society, Baobab for Women’s Human Rights and Action Aid, Project Alert on Violence Against Women, Transition Monitoring Group, Nigerian Women Asusun Amincewa da Dorothy Njemanze Foundation.

Womanifesto ta ce ta yi matuƙar kaɗuwa da ƙisan rashin adalci da aka yi wa Raheem, ta kuma yi kira ga gwamnatin jihar Legas da rundunar ‘yan sandan Najeriya da su gurfanar da ASP Drambi Vandi a gaban kuliya.

Sanarwar ta ce, “Muna kira da a gudanar da bincike cikin gaggawa, tsantsar gaskiya da kuma sanya ido.

Wannan ire iren kisa ne da yawa da jami’an ‘yan sanda suka yi. Ƙundin tsarin mulkin Najeriya ya ya yi bayani a fili a kan ‘yancin rayuwa na ‘yan ƙasa a matsayin wani muhimmin haƙƙii na ɗan Adam wanda wani ba zai iya ɗaukar rai ba, ba bisa ƙa’ida ba, kuma doka ta kare haƙƙin rayuwa.

“‘Yan sandan Najeriya na yawan amfani da ƙarfi da bindigogi ba bisa ka’ida ba.

“Yin amfani da ƙarfi ba bisa ka’ida ba barazana ce ga rayuwa, ’yanci, tsaro da kuma kariya daidai gwargwado a karƙashin doka.

“Yana da mahimmanci a lura cewa akwai ƙaƙƙarfan ƙa’idodin ƙasa da ƙasa waɗanda ke tafiyar da yadda, da kuma lokacin da ‘yan sanda za su iya amfani da ƙarfi, ko bindigogi; ɗaya daga ciki shi ne ka’idojin Majalisar ɗinkin Duniya kan amfani da ƙarfi da bindigogi da jami’an tsaro ke amfani da su wanda ya ce jami’an ‘yan sanda su yi amfani da muggan makamai ko bindigogi a matsayin mafita ta ƙarshe kuma idan irin wannan ƙarfi ya zama tilas don kare kansu daga hatsarin da ke tafe, rauni da lokacin da babu makawa sai sun yi hakan.

“Kisan Omobolanle abu ne da za a iya kaucewa ko hana faruwar shi.

“Ta yaya za mu tabbatar da wajabcin kashe wata mace mai ciki wadda ta haifi ‘ya’ya biyar da wasu ‘yan uwa a cikin abin hawa?

“Wannan mutuwa ɗaya ce daga cikin yawa da ke faruwa a Najeriya, wajibi ne hukumomin jihohi ciki har da ‘yan sanda su mutunta rai da kuma kare rai ba tare da nuna bambanci ba don haka dole ne rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ɗaukin mutuwar da wasu ire iren ta da dama.

“Dole ne su kawo ƙarshen zalunci da cin zarafi da ‘yan sanda ke yi da gangan waɗanda babban take hakkin ɗan Adam ne” in ji ƙungiyoyin matan.

Sashe na 222 da 223 na dokar laifuka ta jihar Legas (2015) a fili sun bayyana ƙisan kai a matsayin babban laifi da kuma tsara hukuncinsa, sashi na 73 yayi magana akan laifin cin zarafin mulki.

Laifin ASP Drambi Vandi ya tauye ‘yancin rayuwar Omobolanle, ya kuma tauye wa danginta jin daɗin rayuwa.

“A matsayinmu na kungiya, mun ƙuduri aniyar haɗaka da wasu ‘yan Najeriya musamman ƙungiyar lauyoyin Najeriya, domin tabbatar da cewa muna tafiya tare da iyalai da ‘yan Najeriya masu jahar cewa don ganin an yi adalci, muna jajanta wa dangi yayin da muke buƙatar cikakken gyare-gyaren a tsarin ‘yan sanda wanda ke da ɗorewa kuma mai fa’ida ga tsaron jama’a.” In ji su.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like