Connect with us

Labarai

Manoma a Maiduguri sun roƙi sojoji da su ƙara musu wa’adin aikin gona

Published

on

Manoman da ke kan titin Maiduguri- Damboa-Biu da ke wajen birnin Maiduguri a ranar Alhamis sun yi ƙira ga sojoji da su sake duba lokacin da aka basu na damar yin aiki a gonakinsu.

Da dama da suka zanta da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a Maiduguri sun ce ƙarfe 11 na safe zuwa ƙarfe 4:00 na yamma, lokacin da aka ba su damar ya kamata a faɗaɗa kuma a ƙara yawan adadin manoma.

“Jami’an tsaro sun ba da katin shiga ga manoma kaɗan, kuma in ba ka da kati, babu manomi da zai iya shiga gonarsa.

KU KUMA KARANTA: Gwamnati ta sasanta tsakanin manoma da makiyayan masarautar Kaltungo a jihar Gombe

“Abin da muke so shi ne a bar manoma da yawa sannan kuma a faɗaɗa lokacin domin manoma su riƙa zuwa gonaki tsakanin ƙarfe 8 na safe da ƙarfe 6 na yamma, ”Abdullahi, wani manomi ya shaida wa NAN.

Abdullahi, ya yabawa jami’an tsaro kan inganta tsaro a yankin. Ya ce hanya mafi dacewa da za a bi domin ganin an inganta harkokin tsaro da kuma sauƙaƙa dawowar al’amura shi ne a sassauta tsauraran matakan tsaro yayin da aka samu sauƙi.

Wani manomi mai suna Malam Modu, ya ce manoman sun damu da yadda makiyaya ke kiwo a gonakinsu da kuma rashin su musamman a lokacin girbi.

“An ce mu bar gonakin da ƙarfe 4 na yamma, sai dai ka yi mamaki yadda a wasu lokuta ake barin wasu makiyaya su yi kiwo a amfanin gonakin mu.

“Lokacin da aka taƙaita ayyukan noma, ya kamata kuma a taƙaita kiwo” Modu ya dage.

Babagoni, Haruna da Lazarus, wasu manoma uku sun bayyana cewa, a wata hanya ta hanyar Maiduguri zuwa Damaturu, jami’an soji sun bari a fara noma da ƙarfe 7 na safe, kuma ya kamata su riƙa amfani da hanyar Maiduguri zuwa Biu.

Sun buƙaci da a riƙa yin taro akai-akai tsakanin jami’an tsaro da manoma domin cimma matsaya guda.

“Jami’an tsaro wani lokaci suna ba manoma taƙaitaccen sanarwa don kammala girbin su kuma a cikin haka sai da yawa suka girbe amfanin gona da ba su kai ga yi ba,” in ji Haruna.

Wani jami’in tsaro da ya zanta da NAN bisa sharaɗin sakaya sunansa ya ce dukkanin matakan da aka ɗauka na kare muradun manoma ne.

“Wasu watannin baya babu wanda ya isa ya kuskura ya yi noma a wannan yanki; amma tare da ingantaccen yanayin tsaro, ana barin da yawa damar shiga gonakinsu, amma tare da wasu ƙuntatawa.

“Ya kamata manoma su yi haƙuri. Da lokaci komai zai yi kyau a gare mu duka,” kamar yadda ya shaida wa NAN.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like