Connect with us

Labarai

Majalisar tattalin arziƙi za ta yi aiki da ƙungiyar ƙwadago kan cire tallafin man fetur

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Majalisar Tattalin Arziƙin, wadda mataimakin shugaban ƙasa ke jagoranta, ta ƙunshi gwamnonin jihohin ƙasar 36.
Majalisar kula da Tattalin Arziƙin Najeriya ta ce ta ɗauki wani mataki na tunkarar matsalar cire tallafin man fetur a ƙasar, inda ta kafa wani kwamitin wucin gadi.

Babban manufar kafa kwamitin ita ce fara tattaunawa da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago na jihohi daban-daban don samun mafita.

A yayin taron majalisar karo na 135 a Abuja ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ne aka yanke shawarar kafa kwamitin.

Kwamitin ya ƙunshi shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya, AbdulRahman AbdulRazaq da Gwamnan jihar Anambara, Chukwuma Soludo da Shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, Hope Uzodinma na jihar Imo da Shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP, Bala Mohammed na jihar Bauchi, da gwamnan jihar Abiya, Alex Otti.

KU KUMA KARANTA: Za mu bai wa Google goyon baya don samar da ayyukan yi miliyan ɗaya ga ‘yan Najeriya – Tinubu

Mataimakin shugaban ƙasar ya jaddada cewa aikin kwamitin shi ne haɗa kai da shugabannin ƙungiyar ƙwadago a faɗin Najeriya domin samar da mafita mai amfani ga ƙasar bayan cire tallafin man fetur.

Bugu da ƙari, majalisar ta NEC ta samu bayanai kan yadda ake ci gaba da raba muhimman kayayyaki a faɗin ƙasar baki ɗaya kamar shinkafa da hatsi da takin zamani ga jihohi.

An kuma amince da matakin ba da tallafin kuɗi naira biliyan biyar daga gwamnatin tarayya, tare da jinjina wa babban bankin Najeriya (CBN) da hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) bisa gudunmawar suke takawa game da waɗannan tsare-tsare.

Hukumar ta kuma amince da ƙoƙarin da gwamnatocin jihohi ke yi a nasu aikin, tare da ƙara musu ƙwarin gwiwar faɗaɗa rabon kayan agaji domin rage wahalhalun da ‘yan ƙasa ke ciki musamman talakawa masu ƙaramin ƙarfi.

Majalisar ta kuma miƙa ta’aziyya ga rundunar sojojin Najeriya da iyalansu kan kisan da aka yi wa wasu dakarunta a jihar Neja tare da yin shiru na minti ɗaya don karrama mamatan.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like