Connect with us

'Yansanda

Likitan bogi da ya ɗinke mahaifa da mafitsarar wata mace ya shiga hannu

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Ondo ta cafke wani mutum mai suna Olelekan Rabiu mai shekaru 31 da haihuwa, wanda ake zargi da nuna kansa a matsayin likita kuma babban likitan asibitin Iremide Private, da ke Orita Ojo a ƙaramar hukumar Odigbo ta jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Oyediran Oyeyemi, ya gurfanar da wanda ake zargin tare da wasu mutane uku a gaban manema labarai a ranar Juma’a a garin Akure.

Oyeyemi ya bayyana cewa, a ranar 20 ga watan Disamba ne wata tawagar jami’an ‘yan sanda ta musamman, suka kama wanda ake zargin, a lokacin da aka samu rahoton rashin ɗa’a a kansa.

Kwamishinan ‘yan sandan ya ce wanda ake zargin ya yi wa wata mata mai juna biyu aikin tiyatar (an sakaya sunanta) wadda daga baya aka garzaya da ita asibiti saboda yawan zubar da jini daga al’aurarta.

“An gano cewa likitan da ya bayyana kansa, ya ɗinke mahaifa da kuma wajen fitsari.

“A binciken da ake yi, an gano cewa wanda ake zargin ba likita ba ne, amma ya halarci makarantar fasahar lafiya ta Ijebu-Ode, inda ya yi karatu a matsayin ma’aikacin lafiyar jama’a. “Kuma ya kasance yana yaudarar mutane da cewa shi likita,” in ji shi.

Yayin da yake zantawa da manema labarai, Olalekan Rabiu ya amince cewa shi ma’aikaci ne a fannin kiwon lafiyar al’umma, inda ya ce ya shafe shekaru bakwai yana wannan sana’a.

Ya ce, yayi aikin cikin nasara a lokacin da ya yi wa matar da ake magana a kai, bayan kwana 27 ta dawo ta yi korafin zubar jinin.

Ya ce a baya ya yi aiki guda ɗaya cikin nasara, ya ce ya fara aikin tiyata ne a lokacin da ɗan uwansa ya saya masa gidan sama a shekara 2015.

“A gaskiya, ni ba likita ba ne amma na yi karatu a matsayin ma’aikacin lafiyar jama’a a makarantar lafiya ta Ijebu Ode da ke jihar Ogun.

“Duk da cewa, ina da ƙoƙari a layin kuma babu mai taimako, da zan koma makaranta amma yanzu ina shirin komawa makaranta,” in ji shi.

A cewarsa, an kawo matar asibitisa, wanda yayansa ya sai masa a shekarar 2015, ya ce, bayan da ya duba matar, ya gano cewa ba za a iya haihuwa da kanta ba.

“Bayan na duba lafiyarta, na bayyana wa ‘yan uwanta halin da take ciki, domin na duba sakamakon nata na duban dan tayi na gano tana cikin mako na 43 da ciki.

KU KUMA KARANTA:Hukumar ‘yansanda sun ceto mutane 77 daga coci a Jihar Ondo

Ita ma jaririyar ta riga ta jigata, aka ba ni izinin yi mata tiyata don ceto matar da jaririyar.

“Don haka, lokacin da ta dawo bayan kwana 10,dan na duba lafiyarta, sai na gano cewa ba ta shan magani, kuma ba ta da tsafta.

“Bayan an shafe kwanaki 27 da yi mata tiyata, sai ta sake dawowa tana korafin zubar jini, domin ceto rayuwarta, don haka nan take, na mika ta zuwa cibiyar kula da masu fama da cutar da ke garin Ondo.

Ya ƙara da cewa, “Ina son mutane su taimake ni, ina da mata mai ɗauke da juna biyu na wata tara a gida yanzu, na yi alƙawarin ba zan ƙara ba,” inji likitan bogin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like