Connect with us

Siyasa

Kwankwaso ne kaɗai zai iya fitar da NNPP daga rikici – Masu ruwa da tsaki

Published

on

Yayin da rikicin jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, (NNPP) ke ƙara ta’azzara, masu ruwa da tsaki na ganin cewa Sanata Rabi’u Kwankwaso, ɗan takararta na shugaban ƙasa, shi ne mafi cancantar dawo da zaman lafiya.

Wasu daga cikinsu, waɗanda suka yi magana da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, sun ce Kwankwaso ne shugaban jam’iyyar wanda zai iya kawo ƙarshen wannan mummunar ɗabi’a ta hanyar ƙiran taron dangi cikin sauƙi.

Ku tuna cewa a kwanakin baya jam’iyyar ta tsunduma cikin rikici inda wani ɓangare ya dakatar da Kwankwaso da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar bisa zargin cin zarafin jam’iyyar.

Ƙungiyar ta kuma zarge shi da yin zagon ƙasa da masu adawa da NNPP. Wata ƙungiya yayin da take mayar da martani kan dakatarwar da aka yi wa Kwankwaso, ta kori Dakta Boniface Aniebonam, wanda ya ƙafa jam’iyyar kuma tsohon shugaban kwamitin amintattu.

Yayin da jam’iyyar ke ninƙaya a cikin irin wannan ruɗani, masu ruwa da tsaki sun ba da shawarar a gudanar da taro domin warware batutuwan da kuma tsara hanyar da za a bi.

KU KUMA KARANTA: Ganduje ba zai iya kallon idona kai tsaye ba, ni ubansa ne a siyasa – Kwankwaso

Ɗaya daga cikin masu ruwa da tsaki shi ne Mordekai Ibrahim, ɗan takarar majalisar jiha a jihar Kaduna.

“Sanata Rabi’u Kwankwaso a matsayinsa na shugaban jam’iyyar ya kamata ya ƙira taron da za mu gudanar da bincike a kan zaɓen 2023 mai zuwa.

“Dole ne dukkan ɓangarorin su yi takuba da takubbansu kuma su ba da damar demokraɗiyya ta cikin gida. “Dole ne jam’iyyar ta kawo ƙarshen duk wani nau’in cece kuce.

Dole ne mu yi haƙuri da wuce gona da iri. “Ba wanda yake yaƙar Kwankwaso a NNPP. Dole ne ya yi gaggawar ƙiran taro saboda muna rasa ’yan jam’iya da yawa,” inji shi.

Wani jami’in jam’iyyar na ƙasa, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya yi wannan magana. “Ya kamata Sanata Kwankwaso ya ce wani abu. Shiru ya yi yawa.

Shirun nasa yana shafar numfashin jam’iyyar,” kamar yadda ya shaida wa NAN a wata hira ta wayar tarho. Da aka tuntuɓi Mista Aniebonam ya ce batun batun iyali ne.

“Ina fata Sanata Kwankwaso ya murmure cikin gaggawa daga yanayin da ake iya kaucewa. “Ban yi wani bayani a bainar jama’a kan abubuwan da ke faruwa a jam’iyyar ba, haka ma Kwankwaso.

“Jam’iyyar tana da ’ya’ya maza da ke fafutukar ganin sun dace da kayan ciki, musamman ma membobin kwamitin ayyuka na ƙasa da ba su dace ba.

“Ina sane da cewa Sanata Kwankwaso na iya yin fushi da gaske saboda ya ba da shawara a kan rashin adalcin kungiyar.

“Amma, ina tabbatar muku cewa duk abin da ya faru, NNPP za ta fito da ƙarfi bayan waɗannan yanayi da ake iya kaucewa. “Yana daga cikin siyasa da al’umma kawai.

Abin da ya fi muhimmanci a gare ni da Sanata Kwankwaso a halin yanzu shi ne rigingimun Jihar Kano da kuma ɗora shugabanci na gari,” inji shi. Mista Aniebonam ya buƙaci ‘yan Najeriya da su sanya mutanensa a jam’iyyar NNPP cikin addu’o’i.

“Ina son ‘yan Najeriya su yi addu’a ga Kwankwaso da gwamnan jihar Kano don shawo kan ƙalubalen shugabanci nagari da hassada,” in ji shi.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Kwankwaso zai canza tambarin jam’iyar NNPP | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like