Connect with us

Ƙasashen Waje

Kwamitin Tsaro na MƊD zai kaɗa ƙuri’a kan tsagaita wuta a Sudan gabanin watan Ramadan

Published

on

Kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya zai kaɗa ƙuri’a a ranar Juma’a kan yin kira da a tsagaita wuta a Sudan, a daidai lokacin da za a fara azumin watan Ramadan a mako mai zuwa, yayin da lamura ke ci gaba da taɓarɓarewa a ƙasar.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, daftarin ƙudurin da aka shirya zai yi kira ga dukkan ɓangarorin da su ɗauki matakin dakatar da rikicin ba tare da ɓata lokaci ba kafin watan Ramadan, lokacin da ya kamata ya zama na ibdar azumi da addu’a da tunani ga Musulman duniya.

Har ila yau, ta yi ƙira ga ɓangarorin da ke faɗa da juna da su ba da damar kai agajin jinƙai ba tare da wata tangarda ba ta kan iyakoki da kuma filin daga.

A zaman da kwamitin sulhun ya yi a ranar Alhamis, Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira ga dukkan bangarorin Sudan da su mutunta darajar watan Ramadan ta hanyar dakatar da yaƙi a cikin watan mai alfarma.

KU KUMA KARANTA: Ana yi wa yara fyaɗe sakamakon yaƙin da ke faruwa a Sudan – MƊD

Ya ƙara da cewa, “Dole ne tsagaita wuta ta haɗa da daina ɓrin wuta a duk faɗin ƙasar, tare da samar da tabbatacciyar hanya wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa ga al’ummar Sudan.”

Guterres ya yi gargaɗi game da bala’in jinƙai da ake ciki da kuma ƙaruwar barazanar yunwa.

Daga baya Biritaniya ta sanar da cewa za ta nemi wani ƙuduri da zai sake ɗaukaka ƙorafin nasa.

An fara gwabza yaƙin ne tun ranar 15 ga Afrilun 2023.

An dai yi artabu da sojojin Janar Abdel Fattah al-Burhan da dakarun sa-kai na gaggawa na Janar Mohamed Hamdan Daglo, wanda shi ne na biyu a fagen soja

Hakan ya yi sanadin mutuwar dubban mutane da kuma wasu miliyan takwas da suka rasa matsugunansu, fiye da yadda wani rikici ya jawo a duniya.

Yayin da akasarin mambobin Kwamitin Tsaro a ranar Alhamis suka goyi bayan kiran tsagaita wuta na watan Ramadan, wasu tawagogin sun yi gum da bakinsu, musamman na China da Rasha.

Ita ma Kungiyar Tarayyar Afirka AU a wata sanarwa da ta fitar a yau Juma’a ta kuma yi kira ga ɓangarorin Sudan da ke rikici da juna da su tsagaita wuta a fadin kasar baki daya a cikin watan Ramadan.

Shugaban AU, Moussa Faki Mahamat, ya ce tsagaita wuta na iya taimakawa wajen aikewa da kayan agaji ga fararen hula da ke cikin mawuyacin hali.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like