Connect with us

Labarai

Kotu ta ba da belin Abba Kyari

Published

on

Kotu ta ba da belin Abba Kyari

Kotu ta ba da belin Abba Kyari

Daga Ibraheem El-Tafseer

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da belin DCP Abba Kyari na tsawon makonni biyu bayan ya shafe watanni 27 yana tsare.

Ana sa ran Abba Kyari zai samu damar yin zaman makokin rasuwar mahaifiyarsa, wadda ta a cikin wannan wata na Mayu.

Mahaifiyar ta rasu ne da sanyin safiyar ranar Lahadi, 5 ga Mayu, 2024, kuma ta rasu ta bar ‘ya’ya 10 maza biyar da mata biyar, ciki har da Abba, wanda shi ne babban ɗanta.

Yayin da Abba Kyari bai samu damar halartar jana’izar mahaifiyarsa ba, mazauna jihar Borno sun fito da yawa don yi wa Hajiya Yachilla sutura, wacce tuni aka binne ta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada tun a ranar da ta rasu.

KU KUMA KARANTA: A gabana ‘yan sanda suka kashe makiyaya, bayan Abba Kyari ya nemi in ɗorawa Saraki laifin fashi – Ɗan fashi ga Kotu

Kotun ta sanya ranar Juma’a, 31 ga watan Mayu, domin tantance buƙatar neman belinsa a shari’ar da ake yi kan tuhume-tuhumen da hukumar yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta shigar bayan kama shi shekaru biyu da suka gabata a ranar 14 ga Fabrairu, 2022.

A shekarar 2022, hukumar ‘yan sanda ta dakatar da Abba Kyari da wasu manyan jami’an ‘yansanda biyu – Sunday Ubua da James Bawa – waɗanda ake zargi da hannu a cinikin hodar iblis da ta shafi DCP Abba Kyari

Hukumar ‘yansanda ta dakatar da mataimakin kwamishinan ‘yansanda, ACP Sunday Ubua da mataimakin sufeton ‘yansanda, ASP James Bawa daga gudanar da ayyuka da ayyukan ofisoshinsu daga ranar Litinin, 14 ga Fabrairu, 2022,” in ji PSC. wata sanarwa.

Hukumar NDLEA ta kuma bayyana cewa ana neman Kyari bisa zargin alaƙa da ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ta ƙasa da ƙasa.

Femi Babalola, mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, ya yi zargin cewa Kyari da tawagarsa ta Intelligence Response Team (IRT) sun kama wasu masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka shigo ƙasar daga ƙasar Habasha ɗauke da hodar iblis mai nauyin kilogiram 25, amma sun ɗauki hodar mai nauyin 15kg na kayan da aka kama.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like