Connect with us

Labarai

Kasafin kuɗin 2023: Gwamna Sule zai fara aiki gadan-gadan

Published

on

Gwamnan jihar Nasarawa injiniya Abdullahi Sule ya sanya hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2023 da ya kai sama da naira biliyan 149.3 inda ya ce gwamnati za ta fara aiki ba tare da bata lokaci ba wajen aiwatar da kasafin gaba ɗaya, domin amfanin jihar baki daya.

Kasafin kuɗin, wanda aka yiwa laƙabi da budget of consolidation and continuity, ya an miƙa shi gidan gwamnati Lafia inda gwamnan ya yaba wa kakakin majalisar jihar Ibrahim Balarabe Abdullahi, da ɗaukacin ‘yan Majalisu bisa gaggauta amincewa da takardar bisa kishin da suke da shi ga Jihar.

An gabatar da kasafin kuɗin a zauren majalisar dokokin jihar a ranar 22 ga Nuwamban 2022 kuma ‘yan majalisar suka amince da shi a ranar 20 ga Disamban 2022, gwamna Abdullahi Sule ya bayyana kasafin kuɗi na Naira biliyan 149.3.

KU KUMA KARANTA:Ba zan yi amfani da kuɗin talakawa wajen neman tazarce ba – Abdullahi Sule

Gwamna Sule wanda ya cika da tsare-tsaren da suka kai ga rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗi na ashirin da uku a matsayin doka, ya ci gaba da cewa kasafin kuɗin da aka yi wa lakabi da kasafin bunkasa tattalin arzikin ƙasa da ci gaba, zai baiwa gwamnati damar gudanar da ayyukan da ba su da alaka da gwamnati, samar da shirye-shirye masu dacewa da mutane.

A cewar Gwamnan, tare da ƙudurin tabbatar da ci gaba da tsare-tsare da na gwamnati, ayyukan siyasa da ke gudana ba za su shafi aiwatar da shirye-shiryen gwamnati ba.

Tun da farko kakakin majalisar dokokin jihar Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi ya bayyana cewa, ‘yan majalisar sun tabbatar da cewa ƙudurin kasafin kuɗin ya bi tsarin doka, kafin daga bisani a zartar da shi, don haka ya yaba wa shugabannin ma’aikatun gwamnati da na ƙananan hukumomi da kuma kwamitin kuɗi na majalisar bisa jajircewarsu har zuwa yanzu.

Shugaban majalisar ya kuma yi fatan samun ɗorewar haɗin gwiwa tsakanin ‘yan majalisa da ɓangaren zartaswa na gwamnati a cikin lokaci mai zuwa domin samar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jihar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like