Connect with us

Labarai

Ka riƙa bincike kafin yin magana – Gwamnan Sakkwato ga Shettima

Published

on

Ka riƙa bincike kafin yin magana - Gwamnan Sakkwato ga Shettima

Ka riƙa bincike kafin yin magana – Gwamnan Sakkwato ga Shettima

Daga Muhammad Kukuri

Gwamnatin Sakkwato ta yi martani ga Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima kan kalamansa game da zargin gwamnan jihar da neman tsige Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.

Gwamnatin jihar ta ce ya kamata Shettima ya riƙa bincike ya tabbatar da gaskiya al’amari kafin ya yi tsokaci a kai.

Raddin na zuwa ne bayan gargaɗin da Shettima ya yi wa gwamnatin jihar cewa ta yi hatara da kujerar Sarkin Musulmi saboda muhimmacin matsayin basaraken abu ne da ya kamata duk Najeriya  ta mutunta, ta girmama ta kuma kare ta.

Mataimkain shugaban ƙasar ya yi gargaɗin ne a taron tsaro da zaman lafiya na yankin Arewa maso yamma ranar Litinin a Jihar Katsina inda mataimakin gwamnan Sakkwato ya wakilci Gwamna Ahmad Aliyu.

Aminiya ta ruwaito Ƙungiyar Kare Hakkin Musulmi (MURIC) na zargin Gwamna Ahmad Aliyu da neman tsige Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci a Najeriya, kamar yadda gwamnan ya sauke wasu sarakunan gargajiya 15 a kwanakin baya.

KU KUMA KARANTA:Dole mu kare martabar Sarkin Musulmi – Kashim Shettima

A martanin Gwamna Ahmad Aliyu ga Shettimma, ya buƙaci mataimakin shuganan ƙasar ya riƙa bari sai ya san hakikanin gaskiyar al’amari, musamman wanda ya shafi ƙasa, kafin ya yi magana a kai.

A cikin sanarwar da kakakin gwamnan, Abubakar Bawa, ya sa wa hannu, ya ce, “Mun dauka mataimakin shguaban kasa zai yi hikimar tuntubar gwamna kafin ya yi magana kan lamarin a cikin jama’a.

“A matsayinsa na dattijo kuma uban ƙasa, ya kamata ya bari sai ya samu hujjoji kafin ya yanke hukunci a kan al’amarin da masu neman hana ruwa gudu ke shiryawa musamman a kafofin sada zumunta.

“Gaskiyar lamari ita ce ba mu awa wani shirin tsige Sarkin Musulumi kuma babu barazanar da muka yi masa.

“Sarkin Musulmi na da cikakken iko da ya dace da ofishinsa kuma ba mu taba tauye masa hakki ba.

“Saboda haka maganar a ce mu ba shi kariya da girmamawa ba ta ma taso ba, domin wannan aikimu ne.

“Gwamnati da al’ummar Sakkwato na goyon baya tare da girmma Sarkin Musulmi kuma muna tabbatar wa al’umma cewa za mu ci gaba da yin duk abin da ya dace domin kare Fadar Sarkin Musulmi a kowane lokaci,” in ji sanarwar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like