Connect with us

Labarai

Jihohi Arewa maso yammacin Najeriya sun yi taro kan sauyin yanayi

Published

on

A ci gaba da ɗaukar mataki da ɗan’adam ke yi kan sauyin yanayi da illolinsa, wata ƙungiya, da haɗin gwiwar jihohin arewa maso yammacin Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki, sun haɗu a birnin Kano, don neman mafita ta bai ɗaya.

Batun ɗaukar matakai na bai ɗaya wajen magance matsalolin kwararowar hamada da ƙalubalen muhalli da kiwon lafiya sakamakon sauyin yanayi na cikin ƙudurorin da aka cimma a ƙarshen taron kwamishinonin muhalli da sauyin yanayi na jihohin arewa maso yammacin Najeriya wanda ya wakana a Kano.

Baya ga kwamishinonin kula da al’amuran muhalli da sauyin yanayi daga jihohi 7 na shiyyar arewa maso yamma, taron, wanda ƙungiyar raya muhalli ta surge Africa ta shirya, ya ƙunshi shugabannin kwamitocin majalisun dokoki na waɗannan jihohi masu kula da wannan fanni da sauran masu ruwa da tsaki.

Madam Nasreen Al-Amin daraktar ƙungiyar surge Africa tace “Wannan zance da a ke yi akan sauyin yanayi da kwararowar Hamada muna so a ce ya wuce ƙungiyoyin da ba na gamnati ba ne kawai suke magana akai, muna so a kawo wakilan gwamnati, da sune suke yin doka kuma suke aiwatar da ita”.

KU KUMA KARANTA:Ƙungiyar lauyoyi ta bayyana damuwa kan tauye ‘yancin ba da kariya

A cewar Mahmud Muhammad Abdullahi, guda cikin mahalarta taron kuma kwamishinan raya muhalli na jihar Zamfara, ƙalubalen tsaro da jihar ke fama dashi baya rasa alaka da sauyin yanayi da barazanar kwararowar hamada.

Bakin mahalarta taron dai ya zo wuri guda wajen ganin cewa, ya kamata waɗannan jihohi guda 7 na arewa maso yammacin Najeriya su samar da manufa guda ta yaƙar ƙalubalen da sauyin yanayi ya zo dashi duk kuwa da ‘yan bambamce-bambamcen da ba’a rasa ba a tsakanin su.

Dakta Nura Ibrahim Kazaure shi ne kwamishinan Muhalli na jihar Jigawa, “Ya kamata a ce ko Kano tana yin wani abu na hana sare-saren bishiya ya zama cewa, Jigawa da Kaduna da sauran jihohi sunayi, domin tsarin ya tafi bai ɗaya”.

Kafin cimma wannan manufa, majalisun dokokin jihohin 7 na da gagarumar rawar takawa. Hon Aminu Giɗaɗo shugaban kwamitin kula da harkokin muhalli da sauyin yanayi a majalisar dokoki ta jihar Sokkwato ya fayyace hanyar da za su bi, “Ta hanyar yarda ko amincewa da kasafin daya shafi ayyuka raya muhalli da kuma magance matsalolin da sauyin yanayi kan zuwa da su a kowane lokaci”.

Dama dai manzarta sun daɗe suna bayyana alfanun samar da tsare tsare na bai daya a tsakanin gwamnatocin arewa domin mangance ƙalubalen da yankin ke fuskanta a fannoni daban daban.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like