Connect with us

Labarai

INEC ku sanar da Fintiri a matsayin wanda lashe zaɓen gwamnan Adamawa – PDP

Published

on

Jam’iyyar PDP ta yi ƙira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC da ta dawo da tattara sakamakon zaɓen gwamnan Adamawa tare da bayyana ɗan takarar jam’iyyar Ahmadu Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Jam’iyyar ta yi wannan ƙiran ne a wani taron manema labarai da sakataren yaɗa labaranta na ƙasa, Debo Ologunagba ya yi a Abuja ranar Lahadi. Mista Ologunagba ya ce sakamakon da aka ɗora a tashar INEC, IREv, tuni ya nuna cewa Fintiri ne ya lashe zaɓen.

“Saboda haka PDP ta buƙaci hedikwatar INEC da ta gaggauta umurci jami’in zaɓe da ya kammala tattara sakamakon zaɓe, ya bayyana sakamakon zaɓe a rumfunan zaɓe tare da bayyana ɗan takararmu, Mista Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaɓen, bayan da ya samu rinjayen ƙuri’un da aka kaɗa.

KU KUMA KARANTA: Ramadan: Gwamnatin Kano ta amince da hutun mako 3 ga makarantu

“Daga sakamakon da aka tattara a rumfunan zabe 69 da aka gudanar da zaɓukan ƙarara waɗanda ke kan tashar sakamakon zaɓen INEC (IReV), Fintiri ya lashe zaɓen.

“Don haka jam’iyyarmu ta buƙaci INEC ba tare da ɓata lokaci ba, ta bayyana sakamakon zaɓe kamar yadda aka riga aka tattara daga rumfunan zaɓe sannan ta bayyana Fintiri a matsayin wanda ya yi nasara.

“Duk abin da ya rage daga wannan ba zai samu karɓuwa daga jam’iyyarmu da al’ummar jihar Adamawa ba,” inji shi.

Mista Ologunagba ya yi Allah-wadai da matakin da hukumar zaɓe ta INEC reshen jihar Adamawa, REC, ta ɗauka, a matsayin haramtacce wanda ya tabbatar da zargin da jam’iyyar ta yi a baya na haɗa baki da kuma buƙatar a tsige shi cikin gaggawa.

Ya kuma yi ƙira ga Sufeto Janar na ‘yan sandan da ya gaggauta kamo Yunusa Ari tare da hukunta shi kan yadda doka ta tanada.

“PDP ta lura da shelar da hedikwatar INEC ta yi cewa matakin da Mallam Yunusa Ari ya yi ba shi da wani tasiri.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like