Connect with us

Labarai

Ina marmarin komawa Daura – Shugaba Buhari

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa yana fatan komawa Daura nan da watanni biyar masu zuwa, a ƙarshen wa’adinsa.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Talata ɗauke da sa hannun babban mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan harkokin yaɗa labarai, Garba Shehu, Buhari ya shaida hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin ‘yan ƙungiyar Jam’iyyatu Ansaridden (Attijaniyya) a fadar gwamnati da ke Abuja.

Shugaba Buhari ya godewa ‘ya’yan ƙungiyar bisa gaggarumin addu’o’in da suke yi wa gwamnatinsa da kuma ƙasa, ya kuma yabawa ƙungiyar ta musulunci kan yadda ake ci gaba da yin hakuri akan al’amuran addini a kasar.

KU KUMA KARANTA:Amina Muhammad, Sakatare Janar ta majalisar Ɗinkin Duniya takai ziyara fadar shugaba Buhari

Sanarwar mai taken ‘Shugaba Buhari ya yabawa kungiyar Islama kan yadda suke ƙarfafa haɗin kan addini.

Garba Shehu ya ci gaba da cewa, “Shugaba Buhari wanda ya godewa ‘ya’yan ƙungiyar bisa gaggarumin addu’o’in da suke yi wa gwamnatinsa da kuma ƙasa baki ɗaya , ya ce yana fatan komawa garin Daura nan da watanni biyar masu zuwa a ƙarshen wa’adinsa.

Shugaban ya shaida wa ƙungiyar a ƙarƙashin jagorancin Khalifan Jam’iyyatu Ansarudden (Attijaniyya), Sheikh Muhammad Khalifa Niass, cewa ya yaba da rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya a ƙasashen Afirka da dama.

A yayin ziyarar ban girma da kungiyar ta kai, Sheikh Tijjani Shehul Hadi Almauritany ya gabatar da addu’o’i ga shugaban ƙasa da kuma ‘yan Najeriya yayin da Sheikh Abdullahi Lamine ya gudanar da karatun kur’ani mai tsarki.

A nasa jawabin, Khalifan ƙungiyar, Sheikh Niass, ya ja hankali, kan tarihin Manzon Allah SAW, da irin darussan da musulmi za su iya koya daga tsarin rayuwarsa.

Da yake jaddada wajibcin tuba na gaske, kamar yadda koyarwar Alƙur’ani mai tsarki ta bayyana, Sheikh Niass ya yi alƙawarin cewa ƙungiyar Attijaniyya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai, kamar yadda koyarwar littafi mai tsarki da musulunci suka tanada.

Khalifah Niass ya kuma ba da labarin irin kusancin da mahaifinsa, Sheikh Ibrahim Niass ya ke da ‘yan Nijeriya da al’ummarta, wanda ya kai shekaru saba’in yana mu’amalar arziki da su, inda ya ce iyalansa sun ƙuduri aniyar ci gaba da ƙulla alaƙa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ba zan yi kewar mulki ba – Buhari | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like