Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazan Nijeriya ta ƙaryata zargin bai wa mahajjata abinci kaɗan

Published

on

Hukumar Alhazan Nijeriya ta ƙaryata zargin bai wa mahajjata abinci kaɗan

Hukumar Alhazan Nijeriya ta ƙaryata zargin bai wa mahajjata abinci kaɗan

Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta ƙaryata wani labari da ake ta yaɗawa a shafukan sada zumunta da ake zarginta da bai wa mahajjata abinci ɗan kaɗan.

A ranar Talata ne aka fara yaɗa hoton nau’in abincin karin kumallo da ke nuna kunu kaɗan a wani mazubi da kuma ƙosai ƙwaya uku, inda aka ce wani ɗan jarida ne ya fara yaɗawa don nuna wa duniya yadda ake “bai wa mahajjata abinci kaɗan bayan biyan naira miliyan takwas kuɗin kujerar ajji.”

Lamarin ya jawo Allah wadai a shafukan intanet a Nijeriya, inda aka dinga zargin hukumar da “son wulaƙanta alhazai” kan irin nau’in abincin da take ba su duk da makuɗan kuɗaɗen da suka biya.

Sai dai a sanarwar da ta fitar a ranar Talata da marece mai ɗauke da sa hannun Hajiya Fatima Sanda Usara, mai magana da yawun NAHCON, ta ce “an jawo hankalinmu kan wani labarin ƙarya da shafin Facebook na wani Babagana Digima ya wallafa, da ke nuna wani nau’in abinci da aka ce shi muke raba wa alhazan Nijeriya bayan da suka biya kuɗin kujerar Hajji har naira miliyan takwas.”

KU KUMA KARANTA: Rukunin farko na Alhazan Kano sun tashi zuwa Saudiyya

“Bayan yin abin da ya dace a kan labarin daga tushe mun yi imani cewa dokokin watsa labarai ba su yarda ɗan jarida da ya san abin da yake yi ya dogara da labari daga Facebook kaɗai ba.

Wani abin takaici shi ne cewa ɗan jaridar da ya ɗauki labarin daga Facebook yana nan a Nijeriya bai je Saudiyyan ba,” in ji sanarwar.

NAHCON ta ce da samun labarin ba ta yi ƙasa a gwiwa ba sai ta ja hankalin wanda ya fara ƙirƙirarsa a fili da a bayyane kan rashin sahihancin ikirarin nasa inda ta nemi ya janye zargin, tana mai yi masa uzurin ko bisa rashin sani ya wallafa, amma sai ya ƙi yin hakan.

“Duk da haka alhazai da dama da suke Makkah a halin yanzu sun yi ta ƙaryata zargin nasa ta hanyar wallafa hotunan ainihin abincin da ake ba su a ƙasan labarin da ya wallafa, sannan ma’aikatan NAHCON ma da suke can sun yi bayanin irin abincin da ake bayarwa, suna masu cewa hoton da ya saka din an yi masa kwaskwarima ne, kuma ƙarya ce tsagwaronta.

“Amma duk da haka gidan jaridar Sahara Reporters sun yi biris da hakan.

Kuma jaridar ta yi amfani ne kawai da wani hoto na mahajjatan Babban Birnin Tarayya na abin karyawar da aka ba su a otel ɗinsu a Makkah, amma sai aka yi masa kwaskwarima aka wallafa shi.

A ƙarshe hukumar Alhazan ta yi ƙira ga al’umma da su yi watsi da labarin ƙaryar da ake watsawa a kan batun abin karyawar tana mai nanata cewa ƙarya ce da son ɓata mata suna.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like