Connect with us

Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta ba da hutu ranar Litinin don murnar ranar ma’aikata

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu domin murnar da zagayowar ranar ma’aikata a Nijeriya.

Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya.

Aregbesola, a wata sanarwa ɗauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Shu’aib Belgore, a ranar Juma’a, ya yabawa ma’aikata bisa ƙwazonsu, da sadaukarwa, inda ya bayyana cewa ƙoƙarin da suke yi na da nasaba da ɗaukakar ƙasar nan da kuma girmama Nijeriya yanzu ya yi umarni a cikin kwamiti na al’ummai.

KU KUMA KARANTA: Albufeira, ƙauyen kamun kifin da ya zama baban wurin hutu a duniya

Ya ce, “Akwai mutunci a cikin aiki, dole ne mu kasance da himma da jajircewa kan aikin da muke yi domin yana da muhimmanci ga gina ƙasa.” Ya umurci ma’aikata da su yi koyi da al’adun samar da aiki.

“Ƙarshen aiki shi ne yawan aiki. Yawan aiki ne ke kaiwa ga samar da kayayyaki da ayyuka masu gamsarwa da samar da wadata. Don haka ita ce hanyar samun ci gaban ƙasa da kuma ɗaiɗaikun mutane.”

Ministan ya buƙaci ma’aikata da su ƙara ƙaimi wajen bunƙasa sana’arsu ta hanyar da gwamnatin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ke yi na inganta hanyoyin tafiyar da harkokin mulki da kuma sa ka ɗaukacin al’ummar Nijeriya su samu mafi girman moriyar al’umma.

Ministan ya yabawa dukkanin hukumomin tsaro bisa nasarorin da aka samu wajen yaƙar masu aikata laifuka a faɗin ƙasar nan, domin ya ƙara musu ƙwarin gwuiwa da ka da su yi ƙasa a gwiwa wajen daƙile masu aikata laifuka a duk lokacin da suka ɗaga kai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Gwamnatin Tarayya

Gwamnatina za ta ba da fifiko kan walwalar mata-Tinubu

Published

on

Shugaban ƙasar Najeriya, Bola Tinubu, ya sha alwashin cewar gwamnatinsa za ta ba da fifiko kan walwalar mata da kiyaye haƙƙoƙinsu tare da bunƙasa rayuwarsu.
A sanarwar da hadiminsa akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale ya fitar game da zagayowar ranar mata ta duniya, Tinubu ya bayyana mata a matsayin ƙashin bayan ci gaban kowace al’umma.

Shugaban ƙasar wanda ya fayyace irin rawar da mata ke takawa wajen gina al’umma, ya jaddada cewar, babu shakka, matan Najeriya sun ba da gudunmowa wajen bunƙasa, ci gaba da kuma ɗaukakar ƙasar.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Najeriya za ta fara amfani da kimiyyar zamani wajen fuskantar ‘yan bindiga

A cewar sanarwar, “Shugaba Tinubu ya ba da tabbacin cewar a kowane ɓangare na ci gaban ɗan adam, irin zarar da matan Najeriya suka yi shaida ce ta jajircewa da ƙarfin hali da fikira ta dukkanin matan duniya, kuma wata alama ce ta nagartaccen wakilci na kyakkyawan fata da wanzuwar al’amura.

Tinubu ya ƙara da cewar, taken bikin ranar mata ta duniya na bana na, “a zuba jari a mata domin hanzarta ci gaba”, ya dace da manufofin da gwamnatinsa ta ƙirƙira akan ilimi da baiwa mata tallafi, ba wai kawai ta hanyar shigo da su a harkar mulki ba, harma da tabbatar da cewa sun ci gaba da zama murya mai mahimmanci a fannin ci gaba a dukkanin ɓangarorin tattaliin arziƙi.

Hakazalika Shugaba Tinubu yace, “gwamnatinsa ta maida hankali wajen zuba jari a fannin ilmin ‘ya’ya mata, tare da ƙirƙirar tsare-tsaren da za su ƙarfafesu wajen ba da gudunmowa a fannonin ilmi da kimiya da fasaha da bincike da ƙirƙire-ƙirƙiren da za su yi tasiri a nan gaba”.

Continue Reading

Gwamnatin Tarayya

Matakan da gwamnatin Najeriya ta ɗauka na ƙayyade farashi ba zai kawar da yunwa ba – Masana

Published

on

Masana tattalin arziƙi a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin ƙasar ke ɗauka da ƙyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo ƙarshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da buɗe iyakoki domin shigowa da abinci cikin ƙasar ba.

‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin ƙasar.

Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ɗaukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin ƙasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila.

To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati.

KU KUMA KARANTA:Tsadar abinci: Gwamnati za ta fara raba kayan abinci a faɗin Najeriya – Kwamiti

Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai waɗanda ke sayen kayan abinci a ƙauyuka, domin sayarwa da tsada, haka kuma dole a karya farashin kayan masarufi da dawo da darajar Naira.

Ko a makon da ya gabata sai da wata kotun tarayya da ke jihar Legas ta umarci gwamnatin Najeriya da ta ɗauki ƙwararan matakai na kawo ƙarshen hauhawar kayan masarufi na kafa hukumar ƙayyade farashin abinci ta kasa.

Wasu ‘yan Najeriya sun cewa akwai buƙatar gwamnati ta ɗauki mataki na dawo da darajar Naira da bunƙasa noma da tattalin arziƙi dama dawo da tallafin man fetur.

A ɓangarensa dai Farfesan harkar Noma Abubakar Gudigi cewa ya yi akwai matakin da gwamnati ya kamata ta ɗauka na hana manyan ‘yan kasuwa shiga ƙauyuka domin saye kayan gona daga manoma.

Yanzu dai a yayin da gwamnati ta ɗauki matakai na rage farashin kayan abinci, abun jira a gani shi ne ko matakan za su taimaka wajen kawo sauƙi ga ‘yan ƙasa.

Continue Reading

Gwamnatin Tarayya

Da ba a cire tallafin mai ba, da wahalar da za’a sha a Najeriya ta fi ta yanzu – Gwamnatin tarayya

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na Najeriya, Alhaji Mohammed Idris Malagi ya ce, da gwamnati ba ta cire tallafin mai ba da wahalar da ake ciki a ƙasar ta fi haka a yanzu.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake kare matakin gwamnatin ƙasar na cire tallafin mai a yayin wata hira da tashar talabijin ta Channels.

A lokacin jawabinsa na farko bayan rantsuwa, a Abuja, a watan Mayu na 2023, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa babu sauran tallafin mai.

KU KUMA KARANTA: Za’a rufe kasuwar canji a Abuja, har sai abin da hali ya yi

Tun daga lokacin da shugaban ya sanar da janye tallafin man kayayyaki da sauran harkokin rayuwa a Najeriya suke ta tashin gwauron zabo, rayuwa take ta ƙara tsada ga jama’a.

Kafin cire tallafin man ana sayar da lita ɗaya a ƙasar a lokacin a kan naira 189 a watan Mayu, amma bayan sanarwar cirewar farashin ya koma daga naira 650 zuwa sama.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like